unfoldingWord 34 - Yesu ya Koyar da Wassu Labaru

unfoldingWord 34 - Yesu ya Koyar da Wassu Labaru

إستعراض: Matthew 13:31-46; Mark 4:26-34; Luke 13:18-21;18:9-14

رقم النص: 1234

لغة: Hausa

الجماهير: General

فصيل: Bible Stories & Teac

الغرض: Evangelism; Teaching

نص من الإنجيل: Paraphrase

حالة: Approved

هذا النص هو دليل أساسى للترجمة والتسجيلات فى لغات مختلفة. و هو يجب ان يعدل ليتوائم مع اللغات و الثقافات المختلفة لكى ما تتناسب مع المنطقة التى يستعمل بها. قد تحتاج بعض المصطلحات والأفكار المستخدمة إلى شرح كامل أو قد يتم حذفها فى ثقافات مختلفة.

النص

Yesu ya fadi wadansu labaru da yawa game da Mulkin Allah. Misali, yace, "Mulkin Allah kamar kwayar mastad ya ke da wani ya shuka a gonarsa. Kun sani cewa kwayar mastad ita ce mafi kankanta dukka cikin iri."

"Amma sa'anda kwayar mastad ya girma, sai yafi dukkan itatuwan dake gona girma, kuma da girma sosai harma tsuntsaye sukan zo su huta a cikin rassan sa."

Yesu ya sake fadin wani labari, "Za'a kwatanta mulkin Allah da yistin da mace ke kwabawa cikin curin gurasa har sai ya mamaye dukka curin."

Haka kuma mulkin Allah kamar dukiya ce da wani ya boye a wani fage. Wani mutum dabam ya sami dukiyar shi ma ya sake binne ta. Yana cike da murna harma ya je ya sayar da dukkan mallakar sa, ya yi amfani da kudin don ya sayi filin."

"Haka kuma mulkin Allah kamar lu'u lu'u ne mai darajar gaske. Sa'anda dillalin lu'u lu'u ya same ta, sai ya sayar da dukkan mallakar sa ya yi amfani da kudin domin ya saye ta.''

Sa'annan Yesu ya fadi wani labari wa mutane da suke dogara da ayyukan su nagari amma su na raina sauran mutane. Yace, "Mutane biyu suka je haikali don su yi addu'a. Daya mai karbar haraj i ne, dayan kuma shugaban addini ne."

"Shugaban addinin yayi addu'a kamar haka, 'Na gode maka Allah, domin ni ba mai zunubi bane kamar sauran mutane, barayi, marasa adalci, mazinata, ko kuma kamar wancen mai karban haraji.'''

'''Misali, na kan yi azumi sau biyu ko wace mako, nakan kuma baka daya bisa goma cikin dukkan kudi da kayayyakin da na karba."'

"Amma mai karbar harajin ya tsaya nesa da shugaban addini, baya ma duban sama. A maimakon haka, ya dunkula hannu yana buga girjinsa ya yi addu'a, 'Allah, yi mani jinkai domin ni mai zunubi ne.'''

Sai Yesu yace, "Gaskiya nake gaya maku, Allah ya ji addu'ar mai karban harajin nan ya kuma ce da shi adali. Amma bai so addu'ar shugaban addinin nan ba. Allah zai kaskantar da duk mai fahariya, ya kuma daukaka duk wanda ya kaskantar da kansa."

معلومات ذات صلة

كلمات الحياة - GRN لديها رسائل صوتية تبشيرية فى الاف الغات تحتوى على رسائل الكتاب المقدس الرئيسية عن الفداء والحياة المسيحية.

تحميلات مجانية - هنا يمكنك أن تجد نصوص رسائل GRN الرئيسية فى عدة لغات، بالإضافة إلى صور ومواد أخرى مرتبطة، متوفرة للتحميل.

مكتبة GRN الصوتية - المواد التبشيرية و التعليمية للكتاب المقدس الملائمة لإحتياجات الناس و ثقافاتهم متاحة فى أشكال و أنماط عديدة.

Copyright and Licensing - GRN shares it's audio, video and written scripts under Creative Commons

Choosing the right audio or video format - What audio and video file formats are available from GRN, and which one is best to use?