unfoldingWord 40 - An Gicciye Yesu

unfoldingWord 40 - An Gicciye Yesu

เค้าโครง: Matthew 27:27-61; Mark 15:16-47; Luke 23:26-56; John 19:17-42

รหัสบทความ: 1240

ภาษา: Hausa

ผู้ฟัง: General

ประเภท: Bible Stories & Teac

เป้าหมายของสื่อบันทึกเสียง: Evangelism; Teaching

ข้ออ้างอิงจากพระคัมภีร์: Paraphrase

สถานะ: Approved

บทความเป็นแนวทางพื้นฐานสำหรับการแปลและบันทึกเสียงภาษาอื่นๆ ควรดัดแปลงตามความจำเป็นเพื่อให้เข้าใจและเหมาะสมกับวัฒนธรรมและภาษาแต่ละภาษา คำศัพท์และแนวคิดบางคำที่ใช้อาจต้องอธิบายเพิ่มเติม หรือแทนที่ หรือตัดออก

เนื้อหาบทความ

Bayan sojojin sun yi wa Yesu ba'a, sai suka tafi da shi domin su gicciye shi. Suka sa shi ya dauki gicciyen da zai mutu akai.

Sojojin suka kawo Yesu wurin da ake kira, "Kokon kai" suka kafe hannayensa da kafafunsa da kusa akan gicciye. Amma Yesu ya ce, "Uba ka gafarta masu domin basu san abin da suke yi ba." Bilatus ya bada umarni su rubuta, "Sarkin Yahudawa" akan allo su kuma sa shi akan gicciyen, sama da kan Yesu.

Sojojin suka yi kuri'a akan tufafin Yesu. Sa'anda suka yi haka, sun cika wani annabci da ya ce, "Sun raba tufafina a tsakaninsu, suka sa kuri'a akan tufa ta."

Aka gicciye Yesu tsakanin 'yan fashi biyu. Daya daga cikinsu ya yi wa Yesu ba'a, amma dayan ya ce, "Baka da tsoron Allah? mu mun yi laifi amma wannan mutumin bashi da laifi." Sa'anan ya ce wa Yesu, "In ka yarda ka tuna da ni a mulkinka." Yesu ya amsa masa. "Yau zaka kasance tare da ni a fiddausi."

Shugbannin Yahudawa da wadansu mutane a cikin taron suka yi wa Yesu ba'a. Suka ce masa, "Idan kai 'Dan Allah ne sauko daga kan gicciyen ka ceci kanka! sa'annan zamu gaskanta ka."

Sai sararin sama na lardin ya yi baki gaba daya, ko da yake da tsakiyar rana ne. Wuri ya zama duhu da tsakar rana, aka kuma ci gaba da duhu har sa'a uku.

Sa'anan Yesu yi kuka, "Ya kare! Uba na bada ruhu na a cikin hannun ka." Sai ya sunkuyar da kansa ya saki ruhunsa. Da ya mutu an yi girgizar kasa, sai babban labulen da ya raba mutane da Allah a Haikali, ya tsage biyu, daga sama zuwa kasa.

Ta wurin mutuwarsa, Yesu ya bude hanya da mutane za su zo gun Allah. Da sojan nan mai tsaron Yesu ya ga dukkan abubuwan da suka faru, sai ya ce, "Hakika, wannan mutumin marar laifi ne. Shi Dan Allah ne."

Sa'annan Yusufu da NIkodimas, shugabannin Yahudawa biyu wadanda suka gaskanta, Yesu Almasihu ne, suka tambayi Bilatus jikin Yesu. Suka nade jikinsa cikin zani suka sa shi cikin kabarin dutse da aka sassaka. Sa'anan suka mirgina babban dutse a bakin kabarin domin su rufe kofar.

ข้อมูลที่เกี่ยวข้อง

สื่อบันทึกเสียงรูปแบบmp3, ซีดี, เทปคาสเซ็ท - องค์กรจีอาร์เอ็น มีสื่อบันทึกเสียงต่างๆ หลายพันภาษา เนื้อหาสื่อบันทึกเสียงตรงกับความจริงในพระคัมภีร์ เป็นเรื่องราวเกี่ยวกับความรอดและชีวิตคริสเตียน

ดาวน์โหลดฟรี - ที่นี่ท่านสามารถค้นหาบทความต่างๆ ของจีอาร์เอ็นในภาษาต่างๆ พร้อมทั้งภาพประกอบ และสื่ออื่นๆ ที่สามารถดาวน์โหลดได้

ห้องสมุดสื่อบันทึกเสียงข่าวประเสริฐของจีอาร์เอ็น - เจ็ดสิบกว่าปีที่นักบันทึกเสียงขององค์กรจีอาร์เอ็นได้บันทึกเสียงภาษาของชนกลุ่มน้อยต่างๆ และได้ผลิตสื่อบันทึกเสียงข่าวประเสริฐมากมาย

Choosing the audio or video format to download - What audio and video file formats are available from GRN, and which one is best to use?

Copyright and Licensing - GRN shares it's audio, video and written scripts under Creative Commons