unfoldingWord 43 - Ikkilisiya ta Fara

unfoldingWord 43 - Ikkilisiya ta Fara

Outline: Acts 1:12-14; 2

Script Number: 1243

Language: Hausa

Audience: General

Genre: Bible Stories & Teac

Purpose: Evangelism; Teaching

Bible Quotation: Paraphrase

Status: Approved

Scripts are basic guidelines for translation and recording into other languages. They should be adapted as necessary to make them understandable and relevant for each different culture and language. Some terms and concepts used may need more explanation or even be replaced or omitted completely.

Script Text

Bayan da Yesu ya koma sama, almajiran suka zauna a Urushalima kamar yadda Yesu ya umarce su su yi. Masu bi a can su kan taru kowane lokaci domin addu'a.

Kowace shekara, kwanaki 50 bayan idin ketarewa, Yahudawa sun kan yi bukin wata muhimmiyar rana da ake kira fentikos, Fentikos rana ce da Yahudawa ke bukin girbin alkama. Yahudawa su kan zo daga ko ina a fadin duniya zuwa Urushalima domin su yi bukin fentikos tare. A wannan shekara, bukin fentikos ya zo ne sati guda bayan Yesu ya koma sama

Sa'adda masu bi dukka suke tare a wuri guda, nan da nan sai gidan da suke ciki ya cika da wani kara kamar iska mai karfi. Sai wani abu kamar harshen wuta ya bayyana a bisa kan dukkan masu bi. Suka cika da Ruhu Mai Tsarki, sai suka fara magana da wadansu harsuna.

Da mutanen da ke cikin Urushalima suka ji hargowar, taron jama'a suka zo su ga abin da ke faruwa. Da suka ji masu bi suna furta ayyukan al'ajibai da Allah ya yi, suka yi mamaki kwarai domin suna jin wadannan abubuwa a harsunansu.

Wadansu daga cikin mutanen suka zargi almajiran cewa a buge suke. Amma Bitrus ya tashi tsaye ya ce masu, ''Ku saurare ni, wadannan mutane ba a buge suke ba! Wannan ya cika annabcin da annabi Yowel ya yi, in da Allah ya ce, 'A kwanakin karshe zan zubo da Ruhu na.'''

"Mutanen Isra'ila, Yesu mutun ne da ya yi manyan alamu da al'ajibai ta wurin ikon Allah, kamar yadda kuka gani kuka kuma sani. Amma kuka gicciye shi."

"Ko da shike Yesu ya mutu, Allah ya tashe shi daga matattu. Wannan ya cika annabcin da ya ce, 'Ba zaka bar Mai Tsarkinka ya rube a kabari ba.' Mu, shaidu ne ga wannan tabbataccen al'amarin nan cewa Allah ya tada Yesu daga matattu."

"An daukaka Yesu yanzu zuwa hannun dama na Allah Uba. Yesu kuma ya aiko Ruhu Mai Tsarki, kamar yadda ya alkawarta zai yi. Ruhu Mai Tsarki ne yake sa wadannan abubuwan da kuke gani, kuke kuma ji."

"Kun gicciye mutumin nan, Yesu. Amma ku sani hakika cewa Allah ya maishe shi Ubangiji da kuma Almasihu!"

Mutanen da ke sauraron Bitrus suka damu kwarai domin abubuwan da ya fada. Sai suka tambayi Bitrus da almajiran, "Yan'uwa, me za mu yi?"

Bitrus ya amsa masu, ''Kowannen ku ya tuba a kuma yi masa baftisma cikin sunan Yesu Almasihu domin Allah ya gafarta maku zunuban ku. Sa'annan zai baku kyautar Ruhu Mai Tsarki.''

Kimanin mutane 3,000 ne suka gaskanta da maganan da Bitrus ya yi, suka kuma zama almajiran Yesu. Aka yi masu baftisma suka zama 'yan ikkilisiyar da ke Urushalima.

Almajiran suka ci gaba da jin koyarwar manzanni, suna tare kowane lokaci, suna ci tare, suna addu'a tare, suna jin dadin yabon Allah tare, suna yin komai tare, suna kuma rarraba kome da suke da shi tare. Kowa na tunani mai kyau akan su. A kowace rana ana samun karin mutane masu bada gaskiya.

Related information

Words of Life - Audio gospel messages in thousands of languages containing Bible based messages about salvation and Christian living.

Free downloads - Here you can find all the main GRN message scripts in several languages, plus pictures and other related materials, available for download.

The GRN Audio Library - Evangelistic and basic Bible teaching material appropriate to the people's need and culture in a variety of styles and formats.

Choosing the audio or video format to download - What audio and video file formats are available from GRN, and which one is best to use?

Copyright and Licensing - GRN shares it's audio, video and written scripts under Creative Commons