unfoldingWord 26 - Yesu ya Fara Aikin Sa, na Bishara

unfoldingWord 26 - Yesu ya Fara Aikin Sa, na Bishara

Đề cương: Matthew 4:12-25; Mark 1-3; Luke 4

Số kịch bản: 1226

ngôn ngữ: Hausa

Khán giả: General

Thể loại: Bible Stories & Teac

Mục đích: Evangelism; Teaching

Trích dẫn Kinh Thánh: Paraphrase

Trạng thái: Approved

Bản văn này là một hướng dẫn cơ bản cho dịch và thu âm trong các ngôn ngữ khác. Nó phải được thích nghi với nền văn hóa và ngôn ngữ để làm cho nó phù hợp với từng khu vực, nơi nó được sử dụng khác nhau. Một số thuật ngữ và khái niệm được sử dụng có thể cần một lời giải thích đầy đủ hơn hoặc thậm chí bị bỏ qua trong các nền văn hóa khác nhau.

Kịch bản

Bayan ya yi nasara da jarabobin Shaidan, Yesu ya dawo cikin ikon Ruhu Mai Tsarki zuwa yankin Galili inda ya zauna. Yesu ya tafi wurare dabam dabam yana koyarwa. Kowa ya fadi abu mai kyau game da shi.

Yesu ya tafi garin Nazaret, in da ya zauna yayi yarantakar sa. A ranar Asabar ya tafi masujada. Sai aka mika mashi littafin annabi Ishaya domin ya karanta daga ciki. Yesu ya bude littafin ya kuma karanta wa mutane daga wani sashi.

Yesu yayi karatu, "Allah ya bani Ruhun sa, domin in yi shailar bishara ga talakawa, 'yanci ga daurarru, gani ga makafi, saki ga wadanda aka danne. Wannan ita ce shekarar alheri ta Ubangiji."

Sa'annan Yesu ya zauna. Kowannen su, suka zuba masa ido sosai. Suna sane da sashin nassin da ya karanta na magana ne game da Almasihu. Yesu ya ce, "Kalmonin da na karanta maku suna faruwa yanzu.'' Dukkan mutanen suka yi mamaki. Suka ce, ''Ashe wannan ba 'dan Yusufu bane?''

Sa'annan Yesu ya ce, "Gaskiya ne,ba annabin dake samun karbuwa a garinsa. A lokacin annabi Iliya akwai gwauraye da yawa a Isra''ila. Amma da ba'a yi ruwan sama na shekaru uku da rabi, Allah bai aiki Iliya ya taimaki wata gwauruwa daga Isra'ila ba, amma ya ga wata gwauruwa daga wata al'umma dabam."

Yesu ya ci gaba da cewa, "A lokacin annabi Ilisha, akwai mutane da yawa masu cututtukar fata. Amma Ilisha bai warkar da ko dayansu ba. Ya warkar da cutar fatar Na'aman kadai, shugaban rundunar magabtan Isra'ila.'' Mutanen dake sauraron Yesu Yahudawa ne. Da suka ji ya ce haka, sai suka husata sosai akan sa.

Mutanen Nazaret suka ja Yesu daga masujadar, suka kai shi karshen wani tudu domin su jefar dashi da niyyar su kashe shi. Amma Yesu ya ratsa ta tsakiyar su ya bar garin Nazaret.

Sa'annan Yesu ya bi dukkan yankin Galili, taron jama'a suka zo wurin sa. Suka kawo mutane dayawa marassa lafiya, nakasassu, tare da makafi, da guragu, kurame, da bebaye, sai Yesu ya warkar da su.

Aka kawo wa Yesu mutane da yawa masu aljannu. Ta wurin umarnin Yesu, aljannun suka fita daga cikin mutanen, yawancin lokaci sukan yi ihu, ''Kai 'Dan Allahne!'' Taron mutanen suka yi mamaki, suka yi wa Allah sujada.

Sa'annan Yesu ya zabi mazaje goma sha biyu, wadanda ya kira su manzannin sa. Manzannin suka yi tafiya tare da Yesu suna koya daga gare shi.

Thông tin liên quant

Lời Sự Sống - GRN có lưu trữ hàng ngàn thu âm của các lời dạy Phúc Âm bằng các thứ tiếng khác nhau bao gồm từ những thông điệp cơ bản từ Kinh thánh

Tài liệu miễn phí - Tại đây bạn có thể tìm thấy các thông điệp chính của GRN bằng các thứ tiếng khác nhau bao gổm cả hình ảnh và các tài liệu khác có liên quan có thể tải xuống được

Thư viện âm thanh của GRN - Các tài liệu giảng dạy Kinh Thánh cơ bản và nâng cao phù hợp với nhu cầu và văn hóa của mọi người, đa dạng về cả hình thức và phong cách

Copyright and Licensing - GRN shares it's audio, video and written scripts under Creative Commons

Choosing the right audio or video format - What audio and video file formats are available from GRN, and which one is best to use?