unfoldingWord 06 - Allah ya Tanada wa Ishaku
Đề cương: Genesis 24:1-25:26
Số kịch bản: 1206
ngôn ngữ: Hausa
Khán giả: General
Thể loại: Bible Stories & Teac
Mục đích: Evangelism; Teaching
Trích dẫn Kinh Thánh: Paraphrase
Trạng thái: Approved
Bản văn này là một hướng dẫn cơ bản cho dịch và thu âm trong các ngôn ngữ khác. Nó phải được thích nghi với nền văn hóa và ngôn ngữ để làm cho nó phù hợp với từng khu vực, nơi nó được sử dụng khác nhau. Một số thuật ngữ và khái niệm được sử dụng có thể cần một lời giải thích đầy đủ hơn hoặc thậm chí bị bỏ qua trong các nền văn hóa khác nhau.
Kịch bản
Sa'anda Ibrahim ya tsufa sosai, 'dansa, Ishaku, kuwa ya girma ya kai namiji. Sai Ibrahim ya aiki daya daga cikin barorinsa, zuwa kasar da danginsa suke zama domin ya kawo wa dansa, Ishaku, mata.
Bayan tafiya mai nisa zuwa kasar da dangin Ibrahim suke zama, Allah ya bi da baran zuwa wurin Rifkatu. Ita jika ce ga dan'uwan Ibrahim.
Rifkatu kuwa ta yarda ta bar iyalin ta, ta koma tare da baran zuwa gidan Ishaku. Da isar ta kuwa Ishaku ya aure ta.
Bayan tsawon lokaci, Ibrahim ya mutu, sa'annan Allah ya mika wa Ishaku dukkan alkawaran da yayi masa cikin wa'adi. Alkawarin da Allah ya yi wa Ibrahim cewa zai sami iyalai da baza su kidayu ba, amma Rifkatu matar Ishaku bata iya samun 'ya'ya ba.
Sai Ishaku ya yi wa RIfkatu addu'a, Allah kuma ya yarda ta cikin tagwaye. Jariran biyu kuwa suka rika kokawa da juna tun suna cikin Rifkatu, sai Rifkatu ta tambayi Allah me ke faruwa.
Allah ya ce wa Rifkatu, ''Kabilu biyu zasu fito daga ''ya'ya biyun dake cikin ki. Zasu yi fama da juna, sa'annan babban dan zai bauta wa karamin.''
Sa'adda Rifkatu ta haifi 'ya'yan ta, sai babban 'dan ya fito ja da tsuma, sai aka sa masa suna Isuwa. Sai karamin 'dan ya fito yana rike da diddigen Isuwa, aka sa masa suna Yakubu.