unfoldingWord 26 - Yesu ya Fara Aikin Sa, na Bishara

unfoldingWord 26 - Yesu ya Fara Aikin Sa, na Bishara

إستعراض: Matthew 4:12-25; Mark 1-3; Luke 4

رقم النص: 1226

لغة: Hausa

الجماهير: General

فصيل: Bible Stories & Teac

الغرض: Evangelism; Teaching

نص من الإنجيل: Paraphrase

حالة: Approved

هذا النص هو دليل أساسى للترجمة والتسجيلات فى لغات مختلفة. و هو يجب ان يعدل ليتوائم مع اللغات و الثقافات المختلفة لكى ما تتناسب مع المنطقة التى يستعمل بها. قد تحتاج بعض المصطلحات والأفكار المستخدمة إلى شرح كامل أو قد يتم حذفها فى ثقافات مختلفة.

النص

Bayan ya yi nasara da jarabobin Shaidan, Yesu ya dawo cikin ikon Ruhu Mai Tsarki zuwa yankin Galili inda ya zauna. Yesu ya tafi wurare dabam dabam yana koyarwa. Kowa ya fadi abu mai kyau game da shi.

Yesu ya tafi garin Nazaret, in da ya zauna yayi yarantakar sa. A ranar Asabar ya tafi masujada. Sai aka mika mashi littafin annabi Ishaya domin ya karanta daga ciki. Yesu ya bude littafin ya kuma karanta wa mutane daga wani sashi.

Yesu yayi karatu, "Allah ya bani Ruhun sa, domin in yi shailar bishara ga talakawa, 'yanci ga daurarru, gani ga makafi, saki ga wadanda aka danne. Wannan ita ce shekarar alheri ta Ubangiji."

Sa'annan Yesu ya zauna. Kowannen su, suka zuba masa ido sosai. Suna sane da sashin nassin da ya karanta na magana ne game da Almasihu. Yesu ya ce, "Kalmonin da na karanta maku suna faruwa yanzu.'' Dukkan mutanen suka yi mamaki. Suka ce, ''Ashe wannan ba 'dan Yusufu bane?''

Sa'annan Yesu ya ce, "Gaskiya ne,ba annabin dake samun karbuwa a garinsa. A lokacin annabi Iliya akwai gwauraye da yawa a Isra''ila. Amma da ba'a yi ruwan sama na shekaru uku da rabi, Allah bai aiki Iliya ya taimaki wata gwauruwa daga Isra'ila ba, amma ya ga wata gwauruwa daga wata al'umma dabam."

Yesu ya ci gaba da cewa, "A lokacin annabi Ilisha, akwai mutane da yawa masu cututtukar fata. Amma Ilisha bai warkar da ko dayansu ba. Ya warkar da cutar fatar Na'aman kadai, shugaban rundunar magabtan Isra'ila.'' Mutanen dake sauraron Yesu Yahudawa ne. Da suka ji ya ce haka, sai suka husata sosai akan sa.

Mutanen Nazaret suka ja Yesu daga masujadar, suka kai shi karshen wani tudu domin su jefar dashi da niyyar su kashe shi. Amma Yesu ya ratsa ta tsakiyar su ya bar garin Nazaret.

Sa'annan Yesu ya bi dukkan yankin Galili, taron jama'a suka zo wurin sa. Suka kawo mutane dayawa marassa lafiya, nakasassu, tare da makafi, da guragu, kurame, da bebaye, sai Yesu ya warkar da su.

Aka kawo wa Yesu mutane da yawa masu aljannu. Ta wurin umarnin Yesu, aljannun suka fita daga cikin mutanen, yawancin lokaci sukan yi ihu, ''Kai 'Dan Allahne!'' Taron mutanen suka yi mamaki, suka yi wa Allah sujada.

Sa'annan Yesu ya zabi mazaje goma sha biyu, wadanda ya kira su manzannin sa. Manzannin suka yi tafiya tare da Yesu suna koya daga gare shi.

معلومات ذات صلة

كلمات الحياة - GRN لديها رسائل صوتية تبشيرية فى الاف الغات تحتوى على رسائل الكتاب المقدس الرئيسية عن الفداء والحياة المسيحية.

تحميلات مجانية - هنا يمكنك أن تجد نصوص رسائل GRN الرئيسية فى عدة لغات، بالإضافة إلى صور ومواد أخرى مرتبطة، متوفرة للتحميل.

مكتبة GRN الصوتية - المواد التبشيرية و التعليمية للكتاب المقدس الملائمة لإحتياجات الناس و ثقافاتهم متاحة فى أشكال و أنماط عديدة.

Copyright and Licensing - GRN shares it's audio, video and written scripts under Creative Commons

Choosing the right audio or video format - What audio and video file formats are available from GRN, and which one is best to use?