Khetha Ulimi

mic

Ukwabelana

Yabelana ngesixhumanisi

QR code for https://globalrecordings.net/script/8191

unfoldingWord 44 - Biturus da Yahaya sun Warkar da wani Bara

unfoldingWord 44 - Biturus da Yahaya sun Warkar da wani Bara

Uhlaka: Acts 3-4:22

Inombolo Yeskripthi: 1244

Ulimi: Hausa

Izilaleli: General

Inhloso: Evangelism; Teaching

Features: Bible Stories; Paraphrase Scripture

Isimo: Approved

Imibhalo ayiziqondiso eziyisisekelo zokuhunyushwa nokuqoshwa kwezinye izilimi. Kufanele zishintshwe njengoba kunesidingo ukuze ziqondakale futhi zihambisane nesiko nolimi oluhlukene. Amanye amagama nemiqondo esetshenzisiwe ingase idinge incazelo eyengeziwe noma ishintshwe noma ikhishwe ngokuphelele.

Umbhalo Weskripthi

Wata rana, Bitrus da Yahaya suna tafiya Haikali. Da suka kusa da kofar shigar Haikalin, suka ga wani gurgu wanda ke rokon kudi.

Biturus ya dubi gurgun ya ce, "Bani da kudin da zan ba ka. Amma zan baka abin da nake dashi. A cikin sunan Yesu, ka tashi ka yi tafiya!"

Nan da nan Allah ya warkar da gurgun, sai ya fara tafiya yana tsalle, ya na yabon Allah. Mutanen da suke harabar Haikalin suka yi mamaki.

Taron jama'a suka zo da sauri don su ga mutumin da aka warkar da shi. Bitrus ya ce masu, "Don me kuke mamakin cewa mutumin nan ya warke? Ba mu warkar da shi da ikon kan mu, ko adalcin mu ba. Maimakon haka, ikon Yesu ne da bangaskiyar da ya bayar ya warkar da mutumin nan."

"Kune wadanda kuka ce wa Gwamnan Roma ya kashe Yesu. Kuka kashe mahaliccin rai. Amma Allah ya tashe shi daga matattu. Ko da yake baku gane abin da kuke yi ba, Allah ya yi amfani da ayyukan ku don Ya cika annabce anabce cewa Almasihu zai sha wahala ya kuma mutu. Saboda haka ku tuba ku juyo ga Allah, domin a wanke zunuban ku."

Shugabannin Haikalin suka husata, da abin da Bitrus da Yahaya suke cewa. Don haka suka kama su, suka sa su cikin kurkuku. Amma mutane da yawa suka gaskanta da sakon da Bitrus ya fada, don haka jimillar mazaje da suka gaskanta da Yesu, ya karu kimanin 5,000.

Washe gari, shugabannin Yahudawa suka kawo Bitrus da Yahaya wurin babban Firist da wassu shugabbannin addini. Suka tambayi Bitrus da Yahaya, "Da wane iko kuka warkar da wannan gurgun mutum?"

Bitrus ya amsa masu, "Wannan mutumin da ke tsaye a gaban ku, ya warke ne ta ikon Yesu Almasihu. Kun gicciye Yesu, amma Allah ya tashe shi da rai! Kuka ki shi, amma ba wata hanyar ceto sai ko ta wurin ikon Yesu!"

Shugabannin suka yi mamaki yadda Bitrus da Yahaya suka yi magana da gabagadi, suna gani su ba kome bane, ba su kuma karantu ba. Amma suka tuna cewa mutanen nan sun kasance tare da Yesu. Bayan da suka tsorata Bitrus da Yahaya, sai suka bar su su tafi.

Ulwazi oluhlobene

Amazwi Okuphila - Imiyalezo yevangeli elalelwayo ngezinkulungwane zezilimi equkethe imiyalezo esekelwe eBhayibhelini mayelana nensindiso nokuphila kobuKristu.

Copyright and Licensing - GRN shares its audio, video and written scripts under Creative Commons

Choosing the audio or video format to download - What audio and video file formats are available from GRN, and which one is best to use?