unfoldingWord 29 - Labarin Bawa Marar Jinkai
خاکہ: Matthew 18:21-35
اسکرپٹ نمبر: 1229
زبان: Hausa
سامعین: General
نوع: Bible Stories & Teac
نفاست: General
مقصد: Evangelism; Teaching
بائبل کا اقتباس: Paraphrase
حالت: Approved
اسکرپٹ دوسری زبانوں میں ترجمہ اور ریکارڈنگ کے لیے بنیادی رہنما خطوط ہیں۔ انہیں ہر مختلف ثقافت اور زبان کے لیے قابل فہم اور متعلقہ بنانے کے لیے ضرورت کے مطابق ڈھال لیا جانا چاہیے۔ استعمال ہونے والی کچھ اصطلاحات اور تصورات کو مزید وضاحت کی ضرورت ہو سکتی ہے یا ان کو تبدیل یا مکمل طور پر چھوڑ دیا جائے۔
اسکرپٹ کا متن
Wata rana, Bitrus ya tambayi Yesu, "Maigida, sau nawa zan yafe wa dan'uwa na, idan yayi mani laifi? Har sau bakwai?'' Yesu ya ce, "Ba sau bakwai ba, amma saba'in sau bakwai!" Ta haka Yesu, na nufin mu rika yafewa a kowone lokaci. Daga nan Yesu ya bada wannan labarin.
Yesu ya ce, "Mulkin Allah na kama da wani sarki wanda yana son ya daidaita ajiyarsa da barorinsa. Daya daga cikin barorin sa na da bashi mai yawan kimanin albashin shekara 200,000."
“Tunda baran ba zai iya biyan bashinsa ba, sarkin ya ce, 'Ku sayar da mutumin nan da iyalinsa su zama bayi don a sami kudin biyan bashin sa."'
"Baran ya fadi kan gwiwarsa a gaban sarkin ya ce, 'Ka yi mini hakuri zan biya ka dukkan kudin ka da yake na.' Sarkin ya ji tausayin baran, ya share duk bashin sa ya sake shi, ya tafi.”
“Amma da baran nan ya fita daga wurin sarkin, ya ga wani bara dan'uwan sa da yake binsa bashi na misallin albashin wata hudu. Baran nan ya damke dan'uwan sa ya ce, 'Ka biya ni kudin da nake binka!'”
“Dan'uwan sa baran ya fadi akan gwiwar sa, ya ce, 'Ka yi hakuri da ni, zan biya dukkan kudin da kake bi na.' Amaimakon haka baran nan ya jefa dan'uwan sa, kurkuku sai lokacin da zai iya biyan duk kudin da yake binsa.”
“Da wasu barorin sun ga abinda ya faru suka damu kwarai. Suka je wurin Sarki suka gaya masa abin da ya faru.”
“Sarkin ya kira baran ya ce, 'Kai mugun bara! Na yafe maka bashin ka, don ka rokeni. Ai da kaima kayi masa haka.' Sarki ya yi fushi ya kama bawan ya jefa mugun bawan cikin kurkuku har sai ya iya biyan duk kudin da yake bin sa.”
Sa'annan, Yesu ya ce, "Haka Ubana na sama zai yi wa kowane dayan ku, idan ba ku yafe wa dan'uwan ku daga cikin zuciya ba."