unfoldingWord 19 - Annabawa

unfoldingWord 19 - Annabawa

Balangkas: 1 Kings 16-18; 2 Kings 5; Jeremiah 38

Bilang ng Talata: 1219

Wika: Hausa

Tagapakinig: General

Klase: Bible Stories & Teac

Layunin: Evangelism; Teaching

Kawikaan mula sa Bibliya: Paraphrase

Katayuan: Approved

Ang mga script ay panimulang gabay para sa pagsasalin at pagre-record sa ibat-ibang wika.Ang mga ito ay ay dapat na angkupin kung kinakailangan para maunawaan at makabuluhan sa bawat kultura at wika. Ilang termino at konsepto na ginamit ay maaaring gamitin para maipaliwanag o maaari di na palitan o tanggalin ng ganap.

Salita ng Talata

A duk tarihin Isra'ilawa,' Allah ya aika masu annabawa. Annabawan sukan ji sakonni da ga Allah sai fada wa mutane sakonnin Allah.

Iliya annabi ne lokacin da Ahab yake sarki bisa mulkin Isra'ila. Ahab mugun mutum ne wanda ya iza mutane su bauta wa allahn karya, da ake kira Ba'al. Iliya ya ce wa Ahab, "Ba za a yi ruwa ko raba a mulkin Isra'ila ba sai a fada ta." Wannan ya sa Ahab ya yi fushi kwarai.

Allah ya ce wa Iliya ya tafi wani rafi cikin jeji ya boye daga Ahab wanda yake so ya kashe shi. Kowacce safiya da kowacce yammaci, tsuntsaye za su kawo masa gurasa da nama. Ahab da sojojinsa suka nemi Iliya amma basu iya samunsa ba. Farin ya yi tsanani har a karshe rafin ya bushe.

Sai Iliya ya tafi wata makwabciyar kasa. Wata gwauruwa da danta a kasar abincinsu ya kusa karewa saboda rashin ruwan sama ya kawo fari. Amma suka lura da Iliya, Allah kuma ya tanada masu, har garin tukunyarsu da man kwalbarsu basu kare ba. Sun kasance da abinci dukkan kwanakin farin. Iliya ya zauna can shekaru da dama.

Bayan shekaru uku da rabi, Allah ya gaya wa Iliya ya koma kasar Isra'ila ya yi magana da Ahab domin zai aiko da ruwan sama kuma. Da Ahab ya ga Iliya ya ce, "Gaka nan, mai tada hankali!" Iliya ya amsa masa ya ce, "Kai ne mai tada hankali! Ka yashe da Yaweh Allahn gaske, ka yi wa Ba'al sujada. Kawo dukkan mutanen kasar Isra'ila zuwa Dutsen Karmel"

Dukkan mutanen kasar Isra'ila, har ma da annabawan Ba'al 450, suka zo Dutsen Karmel. Iliya ya ce wa mutanen, "Har yaushe zaku dinga sauya ra'ainku? Idan Yaweh shine Allah, ku bauta masa! Idan Ba'al Allah ne ku bauta masa!"

Sai Iliya ya ce wa annabawan Ba'al, "Ku yanka sa, ku shirya shi domin hadaya, amma kada ku hura wuta. Nima zan yi haka. Allahn da ya amsa da wuta shine Allah na gaske." Sai firistocin Ba'al suka shirya hadaya, amma basu hura wuta ba.

Sai annabawan Ba'al suka yi addu'a ga Ba'al, "Ka ji mu Ba'al!" Dukkan yini suka yi ta addu'a da kuma ihu, har ma suka yi ta yayanka kansu da wukake, amma babu amsa.

A karshen ranar, Iliya ya shirya hadaya ga Allah. Sai ya ce wa mutanen su zuba ruwa manyan randuna goma sha biyu bisa hadayar har sai naman, da itacen, da kuma kasar dake kewaye da bagaden sun jike gaba daya.

Sai Iliya ya yi addu'a, "Yahweh, Allah na Ibrahim, da Ishaku,da Yakubu, ka nuna mana yau cewa kai ne Allah na Isra'ila, ni kuma bawanka ne. Ka amsa mini domin wadannan mutane, su sani kai ne Allah na gaske."

Nan take wuta ta fado daga sama, ta kone naman da itacen da duwatsun da kurar har ma da ruwan da ke kewaye da bagaden. Da mutanen suka ga haka, suka fadi a kasa, suka ce, "Yahweh shine Allah! Yahweh shine Allah!"

Sai Iliya ya ce, "Kada ku bar ko wani daga annabawan Ba'al ya kubce!" Sai mutanen suka kama annabawan Ba'al suka dauke su daga wurin suka kashe.

Sai Iliya ya ce wa Sarki Ahab, "Koma maza cikin birni domin ruwan sama na zuwa." Bada jimawa ba sai sama ta yi baki aka soma ruwan sama mai karfi. Yahweh ya tsaida fari ya tabbatar da cewa shine Allahn gaske.

Bayan zamanin Iliya, Allah ya zabi wani mutum mai suna Elisha ya zama annabinsa. Allah ya yi al'ajibai masu yawa ta wurin Elisha. Daya daga cikin al'ajiban ya faru ne da Na'aman, shugaban magabta, wanda yake da mummunar ciwon fata. Ya ji labarin Elisha, sai ya tafi ya roki Elisha ya warkar da shi. Elisha ya gaya wa Na'aman ya tsoma kansa sau bakwai a kogin Urdun.

Da fari Na'aman ya yi fushi, ya so ya ki domin ya ga kamar wauta ce. Daga baya ya sauya ra'ayinsa ya tsunduma kansa sau bakwai a kogin Urdun. Da ya fito ana karshe fatarsa gaba daya ta warke! Allah ya warkar da shi.

Allah ya aiki wassu annabawa da yawa. Dukkansu suka gaya wa mutanen su daina bautar gumaku, su fara nuna adalci da jinkai ga wassu. Annabawan sun yi wa mutanen gargadi cewa idan basu bar yin mugunta ba, su soma biyayya da Allah, Allah zai shari'antasu, masu laifi, ya kuma hukuntasu.

Yawancin lokaci mutanen basu yi biyayya da Allah ba. Sau da yawa sukan wulakanta annabawan a wassu lokatan kuma har su kashe su. A wani lokaci an taba sa annabi Irimiya a wata busasshiyar rijiya, aka bar shi ya mutu a wurin. Ya nutse a cikin laka dake kasan rijiyar, amma dai sai sarki ya yi masa jinkai, ya umarci barorinsa su ciro Irimiya daga rijiyar kafin ya mutu.

Annabawan suka cigaba da magana domin Allah, koda shike mutane sun ki su. Suka fadakar da mutane cewa Allah zai hallakar da su idan ba su tuba ba. Suka kuma tunatar da mutane game da alkawarin cewa Almasihu na Allah zai zo.

Katulad na kaalaman

Salita ng Buhay - Ang GRN ay mayroong mensahe sa audio sa libo-libong wika na naglalaman ng mensahe base sa Bibliya tungkul sa kaligtasan at Kristyanong pamumuhay.

Libreng mga download - Dito ay matatagpuan ang lahat ng pangunahing scripts mensahe ng GRN sa ibat-ibang wika, at mga larawan at iba pang katulad na materyales, ay maaari ng i-download.

Ang GRN Aklatang Audio - Pag-eebanghelyo at panimulang kagamitan ng katuruang Bibliya na angkop sa mga pangangailangan at kultura ng mga tao sa isang iba't ibang estilo at mga format.

Copyright and Licensing - GRN shares it's audio, video and written scripts under Creative Commons

Choosing the right audio or video format - What audio and video file formats are available from GRN, and which one is best to use?