unfoldingWord 13 - Alkawarin Allah da Isra'ila

unfoldingWord 13 - Alkawarin Allah da Isra'ila

Balangkas: Exodus 19-34

Bilang ng Talata: 1213

Wika: Hausa

Tagapakinig: General

Klase: Bible Stories & Teac

Layunin: Evangelism; Teaching

Kawikaan mula sa Bibliya: Paraphrase

Katayuan: Approved

Ang mga script ay panimulang gabay para sa pagsasalin at pagre-record sa ibat-ibang wika.Ang mga ito ay ay dapat na angkupin kung kinakailangan para maunawaan at makabuluhan sa bawat kultura at wika. Ilang termino at konsepto na ginamit ay maaaring gamitin para maipaliwanag o maaari di na palitan o tanggalin ng ganap.

Salita ng Talata

Bayan da Allah ya jagoranci Isra'ilawa suka ratsa Jan Teku, Ya jagorance su cikin daji zuwa dutsen da ake kira Sinai. Wannan shine dutsen da Musa ya gani daji na konewa da wuta. Mutanen kuwa suka gina alfarwa a karkashin dutsen.

Allah ya ce wa Musa da kuma jama'ar Isra'ila, "Idan za kuyi biyayya da ni ku kuma kiyaye alkawarina, za ku zama mallaka ta mai tamani, rundunan firistoci, kuma al'umma mai tsarki."

Bayan kwanaki uku, bayan da mutanen suka shirya kansu da ruhaniyarsu, Allah ya sauko a kan dutsen sina'i da aradu, da walkiya, da hayaki da busar kaho mai kara. Musa ne kadai aka yarda ya haura kan dutsen.

Sa'annan Allah ya basu alkawarin, ya ce, "Ni ne Yahweh, Allahn ku, wanda ya cece ku daga bauta a Masar. Kada ku bauta wa wassu alloli."

"Kada ku kera gumaka kuma kada ku bauta masu, domin Ni, Yahweh, Allah mai kishi ne. Kada ku yi anfani da sunana a rainannun al'amura. Ku tabbata kun kebe ranar asabar da tsarki. Saboda haka, ku yi dukkan ayyukanku a kwanaki shida, domin rana ta bakwai ranar hutu ce agare ku da kuma na tunawa da ni."

"Ka girmama mahaifin ka da mahaifiyar ka. Kada ka yi kisa. Kada ka yi zina. Kada ka yi sata. Kada ka yi karya. Kada ka yi sha'awar matar makwabcin ka, gidan sa, ko wani abinda ke mallakarsa."

Sa'annan Allah ya rubuta wadannan dokoki goma akan Alluna guda biyu kuma ya baiwa Musa. Allah kuma ya bada shari'u da dama da kuma ka'idodi da za'a bi. Idan mutane sunyi biyayya da wadannan shari'u, Allah yayi alkawari cewa zai albarkace su ya kuma kare su. Idan suka ki yin biyayya da su kuma Allah zai hukunta su.

Allah ya sake baiwa Isra'ilawa cikakken kwatancin alfarwa da yake so su kera. Ana kiran ta alfarwar saduwa, kuma yana da dakuna biyu, arabe da baban labule. Babban firist ne kadai ke da iznin shiga dakin da ke bayan labulen, domin Allah na kasancewa awurin.

Duk wanda bai yi biyayya da shari'ar Allah ba zai kawo dabba a bagadi dake gaban alfarwa ta saduwa domin hadaya ga Allah. Firist zai yanka dabbar ya kona a kan bagadi. Jinin dabbar da aka yi hadayan zai rufe zunubin mutumin kuma ya tsarkake mutumin a gaban Allah. Allah ya zabi dan'wan Musa, Haruna, da zuriyar Haruna su zama firistocin sa.

Dukkan jama'a suka amince su yi biyayya da Shari'a da Allah ya basu, su bauta wa Allah shi kadai, su kuma kasance mutanensa na musamman. Amma nan bada jimawa ba bayan da suka yi alkawarin yin biyayya ga Allah, sai suka yi mummunar zunubi.

Kwanaki da dama, Musa yana kan dutsen Sina'i yana magana da Allah. Mutanen kuwa suka gaji da jiran dawowarsa. Sai suka kawo ma Haruna zinariya suka roke shi ya kera masu gumaka!

Haruna ya yi gunkin zinariya mai sifar maraki. Mutanen suka fara bautan gumakan suna mika hadayu ga ita! Allah ya husata dasu kwarai domin zunubin su ya kuwa yi shirin hallaka su. Amma Musa yayi addu'a domin su, Allah ya ji addu'ar sa kuma bai hallaka su ba.

Bayanda Musa ya sauko daga dutsen ya ga gunkin, ya husata kwarai har ma ya murguje allunan nan da Allah ya rubuta dokoki goma akai.

Sa'annan Musa ya daka gunkin ya zama gari, ya zuba garin acikin ruwa kuma ya sa mutanen suka sha ruwan. Allah ya aiko da annuba ga mutanen kuma da yawa suka mutu.

Musa ya kera sabon alluna domin dokoki goma maimakon wadanda suka murguje. Sa'annan ya sake haurawa dutsen kuma yayi addu'a Allah ya gafarta wa mutanen. Allah ya saurari Musa ya kuwa gafarta masu. Musa ya sauko daga kan dutsen da sabon alluna dauke da dokoki goma. Sai Allah ya jagoranci isra'ilawa daga dutsen sina'i zuwa yankin kasar alkawari.

Katulad na kaalaman

Salita ng Buhay - Ang GRN ay mayroong mensahe sa audio sa libo-libong wika na naglalaman ng mensahe base sa Bibliya tungkul sa kaligtasan at Kristyanong pamumuhay.

Libreng mga download - Dito ay matatagpuan ang lahat ng pangunahing scripts mensahe ng GRN sa ibat-ibang wika, at mga larawan at iba pang katulad na materyales, ay maaari ng i-download.

Ang GRN Aklatang Audio - Pag-eebanghelyo at panimulang kagamitan ng katuruang Bibliya na angkop sa mga pangangailangan at kultura ng mga tao sa isang iba't ibang estilo at mga format.

Copyright and Licensing - GRN shares it's audio, video and written scripts under Creative Commons

Choosing the right audio or video format - What audio and video file formats are available from GRN, and which one is best to use?