unfoldingWord 25 - Shaidan ya jarabci Yesu
![unfoldingWord 25 - Shaidan ya jarabci Yesu](https://static.globalrecordings.net/300x200/z40_Mt_04_04.jpg)
Muhtasari: Matthew 4:1-11; Mark 1:12-13; Luke 4:1-13
Nambari ya Hati: 1225
Lugha: Hausa
Hadhira: General
Aina: Bible Stories & Teac
Kusudi: Evangelism; Teaching
Nukuu ya Biblia: Paraphrase
Hali: Approved
Hati ni miongozo ya kimsingi ya kutafsiri na kurekodi katika lugha zingine. Yanafaa kurekebishwa inavyohitajika ili kuzifanya zieleweke na kufaa kwa kila utamaduni na lugha tofauti. Baadhi ya maneno na dhana zinazotumiwa zinaweza kuhitaji maelezo zaidi au hata kubadilishwa au kuachwa kabisa.
Maandishi ya Hati
![](https://static.globalrecordings.net/300x200/z40_Mt_04_01.jpg)
Nan da nan bayan an yi wa Yesu baftisma, Ruhu Mai Tsarki ya bishe Yesu zuwa jeji, in da ya yi azumi kwanaki da dare arba'in, sai Shaidan ya zo wurin Yesu ya jarabce shi domin ya yi zunubi.
![](https://static.globalrecordings.net/300x200/z40_Mt_04_02.jpg)
Shaidan ya jarabci Yesu yana cewa, in kai ne dan Allah, ka mai da duwatsun nan gurasa, don ka ci
![](https://static.globalrecordings.net/300x200/z40_Mt_04_03.jpg)
Yesu amsa ya ce, "A rubuce ya ke a kalmar Allah, 'Mutane basu bukatar gurasa kawai don su rayu, amma suna bukatar kowace kalma da Allah yake fada!"'
![](https://static.globalrecordings.net/300x200/z40_Mt_04_04.jpg)
Sa'annan Shaidan ya dauki Yesu ya kai shi saman haikali a wurin da ya fi tsawo duka, ya ce masa, "In kai ne dan Allah ka yi tsalle daga nan zuwa kasa, domin a rubuce yake, 'Allah zai umurci mala'ikunsa su tallafe ka domin kada kafanka ya yi tuntube da dutse.'''
![](https://static.globalrecordings.net/300x200/z40_Mt_04_05.jpg)
Amma Yesu ya amsa wa Shaidan da abinda aka rubuta daga cikin Nassi. Ya ce, "A kalmar Allah, ya umurci mutanensa, 'Kada ku gwada Ubangiji Allahn ku."'
![](https://static.globalrecordings.net/300x200/z40_Mt_04_06.jpg)
Sai Shaidan ya nuna wa Yesu dukkan mulkokin duniya da dukkan daukakarsu kuma ya ce, "Zan baka dukkan wannan, idan ka rusuna ka yi mani sujada."
![](https://static.globalrecordings.net/300x200/z40_Mt_04_07.jpg)
Yesu amsa "Rabu da ni, shaidan! A kalmar Allah ya umurci mutanensa, 'Ku yi wa Ubangiji Allahn ku sujada shi kadai kuma za ku bauta wa"'
![](https://static.globalrecordings.net/300x200/z40_Mt_04_08.jpg)
Yesu bai fada cikin jerabobin Shaidan ba, saboda haka Shaidan ya rabu da shi. Sai mala'iku suka zo suka yi wa Yesu hidima.