unfoldingWord 36 - Sakewar Kamanni
![unfoldingWord 36 - Sakewar Kamanni](https://static.globalrecordings.net/300x200/z40_Mt_17_05.jpg)
План-конспект: Matthew 17:1-9; Mark 9:2-8; Luke 9:28-36
Номер текста: 1236
Язык: Hausa
Aудитория: General
Цель: Evangelism; Teaching
Features: Bible Stories; Paraphrase Scripture
статус: Approved
Сценарии - это основные инструкции по переводу и записи на другие языки. Их следует при необходимости адаптировать, чтобы сделать понятными и актуальными для каждой культуры и языка. Некоторые используемые термины и концепции могут нуждаться в дополнительном пояснении или даже полностью замещаться или опускаться.
Текст программы
![](https://static.globalrecordings.net/300x200/z40_Mt_17_01.jpg)
Wata rana, Yesu ya dauki uku daga cikin almajiransa, Bitrus, Yakubu, da Yahaya. (Almajirin nan mai suna Yahaya ba shine wanda yayi wa Yesu baftisma ba.) Sun hau kan dutse mai tsawo domin su yi addu'a su kadai.
![](https://static.globalrecordings.net/300x200/z40_Mt_17_02.jpg)
Da Yesu yana addu'a, sai fuskarsa tayi annuri (Haske) kamar rana kuma tufafinsa suka zama fari fat, fiye da yadda wani a duniya zai maishe su.
![](https://static.globalrecordings.net/300x200/z40_Mt_17_03.jpg)
Sa'annan Musa da annabi Iliya suka bayyana. Wadannan mutane sun yi zama a duniya daruruwan shekaru kafin lokacin nan. Sun yi magana da Yesu game da mutuwarsa, wanda zai faru ba da dadewa ba a Urushalima.
![](https://static.globalrecordings.net/300x200/z40_Mt_17_04.jpg)
Yayin da Musa da Iliya ke magana da Yesu, Bitrus yace wa Yesu, "Yana da kyau da muke a nan. Bari mu kafa bukkoki uku, daya na ka, daya na Musa, daya kuma na Iliya." Bitrus bai san abinda yake fada ba.
![](https://static.globalrecordings.net/300x200/z40_Mt_17_05.jpg)
Yayin da Bitrus ke magana, girgije mai haske ta sauko ya lullube su sai murya daga girgijen ya ce, "Wannan shine dana wanda nake kauna. Ina farin ciki da shi. Ku saurare shi." Almajiran nan uku suka razana suka fadi kasa.
![](https://static.globalrecordings.net/300x200/z40_Mt_17_06.jpg)
Sai Yesu ya taba su ya ce, "Kada ku ji tsoro. Ku tashi." Sa'anda suka duba kewaye, sai Yesu shi kadai ke wurin.
![](https://static.globalrecordings.net/300x200/z40_Mt_17_07.jpg)
Yesu tare da almajiran nan uku suka sauka daga dutsen. Sai Yesu yace masu, "Kada ku gaya wa kowa abinda ya faru anan tukunna. Bada dadewa ba, zan mutu in kuma sake rayuwa. Bayan haka, zaku iya fada wa mutane."