unfoldingWord 06 - Allah ya Tanada wa Ishaku
Garis besar: Genesis 24:1-25:26
Nombor Skrip: 1206
Bahasa: Hausa
Penonton: General
Genre: Bible Stories & Teac
Tujuan: Evangelism; Teaching
Petikan Alkitab: Paraphrase
Status: Approved
Skrip ialah garis panduan asas untuk terjemahan dan rakaman ke dalam bahasa lain. Mereka harus disesuaikan mengikut keperluan untuk menjadikannya mudah difahami dan relevan untuk setiap budaya dan bahasa yang berbeza. Sesetengah istilah dan konsep yang digunakan mungkin memerlukan penjelasan lanjut atau bahkan diganti atau ditinggalkan sepenuhnya.
Teks Skrip
Sa'anda Ibrahim ya tsufa sosai, 'dansa, Ishaku, kuwa ya girma ya kai namiji. Sai Ibrahim ya aiki daya daga cikin barorinsa, zuwa kasar da danginsa suke zama domin ya kawo wa dansa, Ishaku, mata.
Bayan tafiya mai nisa zuwa kasar da dangin Ibrahim suke zama, Allah ya bi da baran zuwa wurin Rifkatu. Ita jika ce ga dan'uwan Ibrahim.
Rifkatu kuwa ta yarda ta bar iyalin ta, ta koma tare da baran zuwa gidan Ishaku. Da isar ta kuwa Ishaku ya aure ta.
Bayan tsawon lokaci, Ibrahim ya mutu, sa'annan Allah ya mika wa Ishaku dukkan alkawaran da yayi masa cikin wa'adi. Alkawarin da Allah ya yi wa Ibrahim cewa zai sami iyalai da baza su kidayu ba, amma Rifkatu matar Ishaku bata iya samun 'ya'ya ba.
Sai Ishaku ya yi wa RIfkatu addu'a, Allah kuma ya yarda ta cikin tagwaye. Jariran biyu kuwa suka rika kokawa da juna tun suna cikin Rifkatu, sai Rifkatu ta tambayi Allah me ke faruwa.
Allah ya ce wa Rifkatu, ''Kabilu biyu zasu fito daga ''ya'ya biyun dake cikin ki. Zasu yi fama da juna, sa'annan babban dan zai bauta wa karamin.''
Sa'adda Rifkatu ta haifi 'ya'yan ta, sai babban 'dan ya fito ja da tsuma, sai aka sa masa suna Isuwa. Sai karamin 'dan ya fito yana rike da diddigen Isuwa, aka sa masa suna Yakubu.