unfoldingWord 24 - Yahaya ya yi wa Yesu Baftisma
![unfoldingWord 24 - Yahaya ya yi wa Yesu Baftisma](https://static.globalrecordings.net/300x200/z40_Mt_03_08.jpg)
Тойм: Matthew 3; Mark 1; Luke 3; John 1:15-37
Скриптийн дугаар: 1224
Хэл: Hausa
Үзэгчид: General
Төрөл: Bible Stories & Teac
Зорилго: Evangelism; Teaching
Библийн ишлэл: Paraphrase
Статус: Approved
Скрипт нь бусад хэл рүү орчуулах, бичих үндсэн заавар юм. Тэдгээрийг өөр өөр соёл, хэл бүрт ойлгомжтой, хамааралтай болгохын тулд шаардлагатай бол тохируулсан байх ёстой. Ашигласан зарим нэр томьёо, ухагдахууныг илүү тайлбарлах шаардлагатай эсвэл бүр орлуулах эсвэл бүрмөсөн орхиж болно.
Скрипт Текст
![](https://static.globalrecordings.net/300x200/z40_Mt_03_01.jpg)
Yahaya, 'dan Zakariya da Alisabatu, ya yi girma ya kuma zama annabi. Yayi rayuwa cikin jeji, yana cin zuma da fara, ya na kuma sanye da tufafin da aka yi da gashin rakumi.
![](https://static.globalrecordings.net/300x200/z40_Mt_03_02.jpg)
Mutane da dama suka fito zuwa jejin domin su saurari Yahaya. Sai ya yi masu wa'azi, ya na cewa, "Ku tuba domin mulkin Allah ya kusa!"
![](https://static.globalrecordings.net/300x200/z40_Mt_03_03.jpg)
Da mutane suka ji sakon Yahana, da yawa daga cikinsu suka tuba daga zunubansu, sai Yahaya ya yi masu baftisma. Shugabanin addini da yawa suka zo wurin Yahaya domin ya yi masu baftisma, amma basu tuba ko kuma su furta zunubansu ba.
![](https://static.globalrecordings.net/300x200/z40_Mt_03_04.jpg)
Yahaya ya ce wa shugabanin addinin, "Ku macizai masu dafi! Ku tuba ku sake halayen ku. Duk itacen da bata bada 'ya'ya mai kyau ba, za a sare ta a jefa ta cikin wuta." Yahaya ya cika abin da annabawa suka fada, "Duba, na aiko manzo na, a yariga ka gaba, wanda zai shirya hanyar ka."
![](https://static.globalrecordings.net/300x200/z42_Lk_03_06.jpg)
Wassu daga cikin Yahudawan suka tambayi Yahaya ko shi ne Almasihu, Yahaya kuwa ya amsa, "Bani ne Almasihun ba, amma akwai wanda ke biye da ni. Shi mai girma ne, wanda ban isa in kwance takalmansa ba.''
![](https://static.globalrecordings.net/300x200/z43_Jn_01_04.jpg)
Kashe gari, Sai Yesu yazo domin Yahaya ya yi masa baftisma. Da Yahaya ya ganshi, sai ya ce, "Duba! Ga 'Dan Rago na Allah wanda zai kawar da zunuban duniya."
![](https://static.globalrecordings.net/300x200/z40_Mt_03_07.jpg)
Yahaya ya ce wa Yesu, "Ban isa in yi maka baftisma ba. Maimakon haka kaine zaka yi mani baftisma.'' Amma Yesu yace, ''Kayi mani baftisma, domin abin da ya dace ne ayi." Hakanan Yahaya ya yi masa baftisma, ko da shike Yesu bai taba yin zunubi ba.
![](https://static.globalrecordings.net/300x200/z40_Mt_03_08.jpg)
Sa'anda Yesu ya fito daga ruwa, bayan an yi masa baftisma, sai Ruhun Allah ya bayyana a misalin kurciya ya sauko a kansa. A wannan lokaci, muryar Allah yayi magana daga sama, yana cewa, "Kai 'Da na ne wanda nake kauna, ina kuma farin ciki da kai sosai."
![](https://static.globalrecordings.net/300x200/z40_Mt_03_05.jpg)
Allah ya fadawa Yahaya, "Ruhu Mai Tsarki zai sauko kan wani wanda zaka yi masa baftisma. Wannan mutumin shi ne 'Dan Allah." Allah daya ne. Amma da Yahaya ya yi wa Yesu baftisma, ya ji Allah Uba yayi magana, ya ga Allah 'Da, shi ne Yesu, ya kuma ga Ruhu Mai Tsarki.