unfoldingWord 26 - Yesu ya Fara Aikin Sa, na Bishara

unfoldingWord 26 - Yesu ya Fara Aikin Sa, na Bishara

개요: Matthew 4:12-25; Mark 1-3; Luke 4

스크립트 번호: 1226

언어: Hausa

청중: General

장르: Bible Stories & Teac

목적: Evangelism; Teaching

성경 인용: Paraphrase

지위: Approved

이 스크립트는 다른 언어로 번역 및 녹음을위한 기본 지침입니다. 그것은 그것이 사용되는 각 영역에 맞게 다른 문화와 언어로 조정되어야 합니다. 사용되는 몇 가지 용어와 개념은 다른 문화에서는 다듬어지거나 생략해야 할 수도 있습니다.

스크립트 텍스트

Bayan ya yi nasara da jarabobin Shaidan, Yesu ya dawo cikin ikon Ruhu Mai Tsarki zuwa yankin Galili inda ya zauna. Yesu ya tafi wurare dabam dabam yana koyarwa. Kowa ya fadi abu mai kyau game da shi.

Yesu ya tafi garin Nazaret, in da ya zauna yayi yarantakar sa. A ranar Asabar ya tafi masujada. Sai aka mika mashi littafin annabi Ishaya domin ya karanta daga ciki. Yesu ya bude littafin ya kuma karanta wa mutane daga wani sashi.

Yesu yayi karatu, "Allah ya bani Ruhun sa, domin in yi shailar bishara ga talakawa, 'yanci ga daurarru, gani ga makafi, saki ga wadanda aka danne. Wannan ita ce shekarar alheri ta Ubangiji."

Sa'annan Yesu ya zauna. Kowannen su, suka zuba masa ido sosai. Suna sane da sashin nassin da ya karanta na magana ne game da Almasihu. Yesu ya ce, "Kalmonin da na karanta maku suna faruwa yanzu.'' Dukkan mutanen suka yi mamaki. Suka ce, ''Ashe wannan ba 'dan Yusufu bane?''

Sa'annan Yesu ya ce, "Gaskiya ne,ba annabin dake samun karbuwa a garinsa. A lokacin annabi Iliya akwai gwauraye da yawa a Isra''ila. Amma da ba'a yi ruwan sama na shekaru uku da rabi, Allah bai aiki Iliya ya taimaki wata gwauruwa daga Isra'ila ba, amma ya ga wata gwauruwa daga wata al'umma dabam."

Yesu ya ci gaba da cewa, "A lokacin annabi Ilisha, akwai mutane da yawa masu cututtukar fata. Amma Ilisha bai warkar da ko dayansu ba. Ya warkar da cutar fatar Na'aman kadai, shugaban rundunar magabtan Isra'ila.'' Mutanen dake sauraron Yesu Yahudawa ne. Da suka ji ya ce haka, sai suka husata sosai akan sa.

Mutanen Nazaret suka ja Yesu daga masujadar, suka kai shi karshen wani tudu domin su jefar dashi da niyyar su kashe shi. Amma Yesu ya ratsa ta tsakiyar su ya bar garin Nazaret.

Sa'annan Yesu ya bi dukkan yankin Galili, taron jama'a suka zo wurin sa. Suka kawo mutane dayawa marassa lafiya, nakasassu, tare da makafi, da guragu, kurame, da bebaye, sai Yesu ya warkar da su.

Aka kawo wa Yesu mutane da yawa masu aljannu. Ta wurin umarnin Yesu, aljannun suka fita daga cikin mutanen, yawancin lokaci sukan yi ihu, ''Kai 'Dan Allahne!'' Taron mutanen suka yi mamaki, suka yi wa Allah sujada.

Sa'annan Yesu ya zabi mazaje goma sha biyu, wadanda ya kira su manzannin sa. Manzannin suka yi tafiya tare da Yesu suna koya daga gare shi.

관련정보

생명의 말씀 - GRN 은 성경에 기반한 구원과 그리스도인의 삶에 대한 수천개의 오디오 복음 메시지를 가지고 있습니다.

무료 다운로드 - 여기에서 다운로드 가능한 여러 언어로 된 주요 GRN 메시지 스크립트, 그림 및 기타 관련 자료를 찾을 수 있습니다.

GRN 오디오 도서관 - 전도와 기본 성경 가르침을 위한 자료는 mp3, CD, 카세트 테이프 형태로 사람들의 필요와 문화에 맞추어졌습니다. 녹음은 성경이야기, 전도 메시지, 말씀 읽기, 노래를 포함하여 다양한 스타일로 구성되었습니다.

Copyright and Licensing - GRN shares it's audio, video and written scripts under Creative Commons

Choosing the right audio or video format - What audio and video file formats are available from GRN, and which one is best to use?