unfoldingWord 14 - Yawo acikin Jeji

unfoldingWord 14 - Yawo acikin Jeji

개요: Exodus 16-17; Numbers 10-14; 20; 27; Deuteronomy 34

스크립트 번호: 1214

언어: Hausa

청중: General

장르: Bible Stories & Teac

목적: Evangelism; Teaching

성경 인용: Paraphrase

지위: Approved

이 스크립트는 다른 언어로 번역 및 녹음을위한 기본 지침입니다. 그것은 그것이 사용되는 각 영역에 맞게 다른 문화와 언어로 조정되어야 합니다. 사용되는 몇 가지 용어와 개념은 다른 문화에서는 다듬어지거나 생략해야 할 수도 있습니다.

스크립트 텍스트

Bayanda Allah ya fada wa isra'ilawa dokokin da yake so su yi biyayya da su a matsayin alkawarin sa da su, suka tafi daga dutsen Sina'i. Allah ya fara jagorar su zuwa yankin kasar alkawari, wanda kuma ake kira kan'ana. Al'amudin girgije na tafiye a gabansu zuwa kan'ana su kuma suna biye da shi.

Allah yayi wa Ibrahim, Ishaku, da Yakubu alkawari cewa zai bada kasar alkawari ga zuri'ar su, amma yanzu akwai kungiyoyin mutane da yawa dake zaune a wurin. Ana kiran su kan'aniwa. Kan'aniwa basu bauta ko su yi biyayya da Allah ba. Suna bautar allolin karya kuma suna yin miyagun abubuwa da yawa.

Allah ya cewa Isra'ilawa, "Lalle ne ku kawar da dukkan Kan'aniwa acikin kasar alkawari. Kada ku yi yarjejjeniyar salama da su kuma kada ku aure su. Lelle ne ku hallakar da dukkan gumakunsu gabaki daya. Idan ba ku yi biyayya da ni ba, zaku bauta ma gumakunsu a maimako na."

Sa'anda Isra'ilawa suka iso gabar Kan'ana, Musa ya zabi mutum goma sha biyu, daya daga kowace kabilar Isra'ila. Ya basu umurni su je lekan asirin kasar su kuma gani yadda ta ke. Su kuma dubi yanayin Kan'aniwa su gani ko suna da karfi ko kasassu.

Mutanen nan goma sha biyu suka yi tafiya cikin Kan'ana kwana arba'in sa'an nan suka komo. Suka fada wa jama'ar, "Kasar na da albarka kuma ga yawan anfani!" Amma goma daga cikin masu lekan asirin suka ce, "Birnin na da karfin gaske kuma mutanen katti ne! Idan muka kai masu hari, tabbas zasu fi karfin mu kuma su kashe mu!"

Nan take Kalibu da Joshua, biyu daga cikin masu lekan asirin, suka ce, "Gaskiya ne mutanen Kan'ana dogi ne kuma karfafa, amma tabbas za mu sha karfin su, Allah zai yi yaki amadadin mu!"

Amma mutanen basu saurari Kalibu da Joshua ba. Suka yi fushi da Musa da Haruna suna cewa, "Me yasa kuka kawo mu wannan mummunar wuri? Da ma mun zauna a Masar maimakon a kashe mu cikin yaki kuma a maida matanmu da yayan mu bayi." Mutanen suna so su zabi wani shugaba dabam wanda zai komar da su Masar.

Allah ya husata kwarai har ma ya zo alfarwar saduwa. Allah yace, "Domin kunyi tawaye agare ni, dukkan mutane zasu yi famar yawo a daji. Banda Joshua da Kalibu, kowane daya dake shekara ashirin ko fiye zai mutu acan kuma ba zai taba shiga kasar alkawarin ba."

Da mutanen suka ji haka, suka tuba don sunyi zunubi. Suka dauki kayan yakinsu suka tafi domin su yaki mutanen Kan'ana. Musa kuwa ya gargade su kada su je domin Allah baya tare da su, amma basu saurare shi ba.

Allah bai tafi tare da su zuwa yakin ba, saboda haka aka yi nasara akan su kuma aka kashe da yawa acikin su. Sa'annan Isra'ilawa suka juya wa Kan'ana baya kuma su ka yi faman yawo a daji har shekaru arba'in.

Cikin shekaru arba'in da mutanen Isra'ila suka yi suna yawo a daji, Allah yana yi masu tanadi. Allah ya basu gurasa daga sama, da ake kira "Manna." Ya kuma aiko da yan tsalwa (wanda suke kananan tsuntsaye) a cikin taronsu domin su sami nama su ci. Cikin dukkan lokacin nan, Allah ya kare kayakinsu da takalmansu daga kodewa.

Allah kuwa cikin al'ajibinsa ya basu ruwa daga dutse. Amma duk da haka, mutanen Isra'ila suka yi gunaguni game da Allah da Musa. Duk da haka, adalcin Allah bisa alkawarinsa ga Ibrahim, da Ishaku da Yakubu bai sake ba.

Wani lokaci sa'adda mutanen suka rasa ruwa, Allah ya ce wa Musa, "Yi magana da dutse, ruwa kuwa zai fito daga ita." Amma Musa bai girmama Allah agaban dukkan mutanen ba ta wurin buga dutsen sau biyu da sanda amaimakon magana da ita. Ruwa kuwa ya fito daga dutsen domin kowa ya sha, amma Allah yana fushi da Musa kuma yace, "Bazaka shiga kasar alkawarin ba."

Bayan da Isra'ilawa suka yi ta zagaya acikin daji har shekaru arba'in, dukkan wadanda suka yi tawaye ga Allah sun mutu. Sa'annan Allah ya jagoranci mutanen zuwa iyakar kasar alkawari kuma. Musa kuwa ya tsufa sosai, sai Allah ya zabi Joshua ya taimake shi da shugabantar mutanen. Allah kuwa yayi wa Musa alkawari da cewa wata rana, zai aiko da wani annabi kamar Musa.

Sa'annan Allah ya ce wa Musa ya haura saman dutsen domin ya kalli kasar alkawarin. Musa kuwa ya kalla kasar alkawarin amma Allah bai yarda masa ya shiga ba. Sa'annan Musa ya mutu, Isra'ilawa kuwa suka yi makokinsa har kwana talatin. Joshua kuwa ya zama sabon shugabansu. Joshua shugaba ne nagari domin ya dogara kuma yana biyayya ga Allah.

관련정보

생명의 말씀 - GRN 은 성경에 기반한 구원과 그리스도인의 삶에 대한 수천개의 오디오 복음 메시지를 가지고 있습니다.

무료 다운로드 - 여기에서 다운로드 가능한 여러 언어로 된 주요 GRN 메시지 스크립트, 그림 및 기타 관련 자료를 찾을 수 있습니다.

GRN 오디오 도서관 - 전도와 기본 성경 가르침을 위한 자료는 mp3, CD, 카세트 테이프 형태로 사람들의 필요와 문화에 맞추어졌습니다. 녹음은 성경이야기, 전도 메시지, 말씀 읽기, 노래를 포함하여 다양한 스타일로 구성되었습니다.

Copyright and Licensing - GRN shares it's audio, video and written scripts under Creative Commons

Choosing the right audio or video format - What audio and video file formats are available from GRN, and which one is best to use?