unfoldingWord 36 - Sakewar Kamanni
概要: Matthew 17:1-9; Mark 9:2-8; Luke 9:28-36
スクリプト番号: 1236
言語: Hausa
観客: General
目的: Evangelism; Teaching
Features: Bible Stories; Paraphrase Scripture
状態: Approved
スクリプトは、他の言語への翻訳および録音の基本的なガイドラインです。スクリプトは、それぞれの異なる文化や言語で理解しやすく、関連性のあるものにするために、必要に応じて適応させる必要があります。使用される用語や概念の中には、さらに説明が必要な場合や、完全に置き換えたり省略したりする必要がある場合もあります。
スクリプトテキスト
Wata rana, Yesu ya dauki uku daga cikin almajiransa, Bitrus, Yakubu, da Yahaya. (Almajirin nan mai suna Yahaya ba shine wanda yayi wa Yesu baftisma ba.) Sun hau kan dutse mai tsawo domin su yi addu'a su kadai.
Da Yesu yana addu'a, sai fuskarsa tayi annuri (Haske) kamar rana kuma tufafinsa suka zama fari fat, fiye da yadda wani a duniya zai maishe su.
Sa'annan Musa da annabi Iliya suka bayyana. Wadannan mutane sun yi zama a duniya daruruwan shekaru kafin lokacin nan. Sun yi magana da Yesu game da mutuwarsa, wanda zai faru ba da dadewa ba a Urushalima.
Yayin da Musa da Iliya ke magana da Yesu, Bitrus yace wa Yesu, "Yana da kyau da muke a nan. Bari mu kafa bukkoki uku, daya na ka, daya na Musa, daya kuma na Iliya." Bitrus bai san abinda yake fada ba.
Yayin da Bitrus ke magana, girgije mai haske ta sauko ya lullube su sai murya daga girgijen ya ce, "Wannan shine dana wanda nake kauna. Ina farin ciki da shi. Ku saurare shi." Almajiran nan uku suka razana suka fadi kasa.
Sai Yesu ya taba su ya ce, "Kada ku ji tsoro. Ku tashi." Sa'anda suka duba kewaye, sai Yesu shi kadai ke wurin.
Yesu tare da almajiran nan uku suka sauka daga dutsen. Sai Yesu yace masu, "Kada ku gaya wa kowa abinda ya faru anan tukunna. Bada dadewa ba, zan mutu in kuma sake rayuwa. Bayan haka, zaku iya fada wa mutane."