unfoldingWord 43 - Ikkilisiya ta Fara

unfoldingWord 43 - Ikkilisiya ta Fara

Schema: Acts 1:12-14; 2

Numero di Sceneggiatura: 1243

Lingua: Hausa

Pubblico: General

Genere: Bible Stories & Teac

Scopo: Evangelism; Teaching

Citazione Biblica: Paraphrase

Stato: Approved

Gli script sono linee guida di base per la traduzione e la registrazione in altre lingue. Dovrebbero essere adattati come necessario per renderli comprensibili e pertinenti per ogni diversa cultura e lingua. Alcuni termini e concetti utilizzati potrebbero richiedere ulteriori spiegazioni o addirittura essere sostituiti o omessi completamente.

Testo della Sceneggiatura

Bayan da Yesu ya koma sama, almajiran suka zauna a Urushalima kamar yadda Yesu ya umarce su su yi. Masu bi a can su kan taru kowane lokaci domin addu'a.

Kowace shekara, kwanaki 50 bayan idin ketarewa, Yahudawa sun kan yi bukin wata muhimmiyar rana da ake kira fentikos, Fentikos rana ce da Yahudawa ke bukin girbin alkama. Yahudawa su kan zo daga ko ina a fadin duniya zuwa Urushalima domin su yi bukin fentikos tare. A wannan shekara, bukin fentikos ya zo ne sati guda bayan Yesu ya koma sama

Sa'adda masu bi dukka suke tare a wuri guda, nan da nan sai gidan da suke ciki ya cika da wani kara kamar iska mai karfi. Sai wani abu kamar harshen wuta ya bayyana a bisa kan dukkan masu bi. Suka cika da Ruhu Mai Tsarki, sai suka fara magana da wadansu harsuna.

Da mutanen da ke cikin Urushalima suka ji hargowar, taron jama'a suka zo su ga abin da ke faruwa. Da suka ji masu bi suna furta ayyukan al'ajibai da Allah ya yi, suka yi mamaki kwarai domin suna jin wadannan abubuwa a harsunansu.

Wadansu daga cikin mutanen suka zargi almajiran cewa a buge suke. Amma Bitrus ya tashi tsaye ya ce masu, ''Ku saurare ni, wadannan mutane ba a buge suke ba! Wannan ya cika annabcin da annabi Yowel ya yi, in da Allah ya ce, 'A kwanakin karshe zan zubo da Ruhu na.'''

"Mutanen Isra'ila, Yesu mutun ne da ya yi manyan alamu da al'ajibai ta wurin ikon Allah, kamar yadda kuka gani kuka kuma sani. Amma kuka gicciye shi."

"Ko da shike Yesu ya mutu, Allah ya tashe shi daga matattu. Wannan ya cika annabcin da ya ce, 'Ba zaka bar Mai Tsarkinka ya rube a kabari ba.' Mu, shaidu ne ga wannan tabbataccen al'amarin nan cewa Allah ya tada Yesu daga matattu."

"An daukaka Yesu yanzu zuwa hannun dama na Allah Uba. Yesu kuma ya aiko Ruhu Mai Tsarki, kamar yadda ya alkawarta zai yi. Ruhu Mai Tsarki ne yake sa wadannan abubuwan da kuke gani, kuke kuma ji."

"Kun gicciye mutumin nan, Yesu. Amma ku sani hakika cewa Allah ya maishe shi Ubangiji da kuma Almasihu!"

Mutanen da ke sauraron Bitrus suka damu kwarai domin abubuwan da ya fada. Sai suka tambayi Bitrus da almajiran, "Yan'uwa, me za mu yi?"

Bitrus ya amsa masu, ''Kowannen ku ya tuba a kuma yi masa baftisma cikin sunan Yesu Almasihu domin Allah ya gafarta maku zunuban ku. Sa'annan zai baku kyautar Ruhu Mai Tsarki.''

Kimanin mutane 3,000 ne suka gaskanta da maganan da Bitrus ya yi, suka kuma zama almajiran Yesu. Aka yi masu baftisma suka zama 'yan ikkilisiyar da ke Urushalima.

Almajiran suka ci gaba da jin koyarwar manzanni, suna tare kowane lokaci, suna ci tare, suna addu'a tare, suna jin dadin yabon Allah tare, suna yin komai tare, suna kuma rarraba kome da suke da shi tare. Kowa na tunani mai kyau akan su. A kowace rana ana samun karin mutane masu bada gaskiya.

Informazioni correlate

The GRN Audio Library - Evangelistic and basic Bible teaching material appropriate to the people's need and culture in a variety of styles and formats.

Copyright and Licensing - GRN shares it's audio, video and written scripts under Creative Commons

Choosing the right audio or video format - What audio and video file formats are available from GRN, and which one is best to use?