Veldu tungumál

mic

unfoldingWord 07 - Allah ya albarkaci Yakubu

unfoldingWord 07 - Allah ya albarkaci Yakubu

Útlínur: Genesis 25:27-35:29

Handritsnúmer: 1207

Tungumál: Hausa

Áhorfendur: General

Tilgangur: Evangelism; Teaching

Features: Bible Stories; Paraphrase Scripture

Staða: Approved

Forskriftir eru grunnleiðbeiningar fyrir þýðingar og upptökur á önnur tungumál. Þau ættu að vera aðlöguð eftir þörfum til að gera þau skiljanleg og viðeigandi fyrir hverja menningu og tungumál. Sum hugtök og hugtök sem notuð eru gætu þurft frekari skýringar eða jafnvel skipt út eða sleppt alveg.

Handritstexti

Sa'anda yayan ke girma, Yakubu yana son zaman gida, amma, Isuwa yana son farauta, Rafkatu tana kaunar Yakubu amma Ishaku yana kaunar Isuwa.

Wata rana, da Isuwa ya dawo daga farauta, yana ji yunwa sosai. Sai ya ce wa Yakubu, "Ba ni daga cikin abincin da ka dafa." Sai Yakubu ya ce masa, "Da farko, ka ba ni matsayinka na dan fari." Sai Isuwa ya ba shi matsayinsa na dan fari. Sa'annan Yakubu ya ba shi abinci.

Ishaku ya so ya ba wa Isuwa albarkarsa. Amma kafin ya yi haka, Rifkatu da Yakubu suka yaudare shi ta wurin sa Yakubu ya badda kamaninsa, kamar shine Isuwa. Ishaku ya tsufa kuma baya ganin. saboda haka, Yakubu ya saka tufafin Isuwa, ya kuma daura fatar akuya a wuyarsa da hannayensa.

Yakubu ya zo wurin Ishaku, ya ce, "Ni ne Isuwa. Na zo domin ka albarkace ni." Da Ishaku ya taba gashin akuyar, ya sunsuna tufafin, sai ya yi tsammanin Isuwa ne, ya kuma albarkace shi.

Isuwa ya ki jinin Yakubu domin ya sace masa damar sa na dan fari, da kuma albarka. Sai ya yi niyyar ya kashe Yakubu bayan mutuwar mahaifinsu

Amma Rifkatu ta ji shirin Isuwa. Sai ita da Ishaku suka tura Yakubu wuri mai nisa, ya zauna da dangin ta.

Yakubu ya zauna da dangin Rifkatu shekaru masu yawa. A wannan lokacin, ya yi aure, ya haifi yaya maza goma sha biyu da ya mace guda daya, Allah ya azurta shi sosai.

Bayan shekaru ashirin da barin gidansa na kan'ana, Yakubu ya komo wurin da iyalinsa, da barorinsa, da dukkan garkin dabbobinsa.

Yakubu ya tsorata sosai domin yana tsamanin har yan zu Isuwa yana so ya kashe shi. Sai ya tura garkunan dabbobi masu yawa kyauta ga Isuwa. Barorin da suka kawo dabbobin suka ce wa Isuwa, "Bawan ka, Yakubu ne, ke baka wadannan dabbobin.Yana zuwa bada jimawa ba.

Amma Isuwa ya rigaya ya yafe wa Yakubu, sun yi murnar sake ganin juna. Sa'annan Yakubu yayi zaman salama a Kan'ana. Sai Ishaku ya rasu, Yakubu da Isuwa suka binne shi. Wa'din alkawaran da Allah ya yi wa Ibrahim ya ci gaba daga kan Ishaku zuwa kan Yakubu.

Tengdar upplýsingar

Orð lífsins - Hljóðboðskapur í guðspjalli á þúsundum tungumála sem inniheldur biblíutengdan boðskap um hjálpræði og kristna lífsstíl.

Choosing the audio or video format to download - What audio and video file formats are available from GRN, and which one is best to use?

Copyright and Licensing - GRN shares its audio, video and written scripts under Creative Commons