unfoldingWord 22 - Haihuwar Yahaya

unfoldingWord 22 - Haihuwar Yahaya

Grandes lignes: Luke 1

Numéro de texte: 1222

Langue: Hausa

Audience: General

Genre: Bible Stories & Teac

Objectif: Evangelism; Teaching

Citation biblique: Paraphrase

Statut: Approved

Les scripts sont des directives de base pour la traduction et l'enregistrement dans d'autres langues. Ils doivent être adaptés si nécessaire afin de les rendre compréhensibles et pertinents pour chaque culture et langue différente. Certains termes et concepts utilisés peuvent nécessiter plus d'explications ou même être remplacés ou complètement omis.

Corps du texte

A zamanin da, Allah yayi magana da mutanensa ta wurin mala'iku da annabawa. Amma shekaru 400 suka wuce da bai yi masu magana ba. Ba labari sai wani mala'ika ya zo da sako daga Allah zuwa warin tsohon firist mai suna Zakariya. Zakariya da matarsa, Alisabatu, mutane masu tsoron Allah ne, amma ba ta iya ta sami yara ba.

Sai mala'kan yace wa Zakariya, "Matar ka zata sami yaro. Za ka sa masa suna Yahaya. Za'a cika shi da Ruhu Mai Tsarki, kuma zai shirya mutane domin Almasihu!" Zakariya ya amsa, "Matata da ni mun tsufa ainun har da zamu sami yara! Yaya zan san wannan zai faru?"

Sai mala'ikan ya amsa wa Zakariya, "Allah ne ya aiko ni, in kawo maka wannan labari mai dadi. Saboda ba ka gaskanta da ni ba, ba zaka iya yin magana ba har sai an haifi yaron. "Nandanan Zakariya ya kasa yin magana. Sai mala'ikan ya bar Zakariya. Bayan wannan, Zakariya ya koma gida matarsa kuma ta sami ciki.

Sa'anda Alisabatu tana da ciki wata shida, wannan Mala'ikan ba zato ya sake bayyana ga `yar'uwar Alisabatu wanda sunanta Maryamu. Ita budurwa ce wadda ke da alkwarin aure da wani nutum mai suna Yusufu. Sai mala'ikan ya ce, "Za ki yi ciki kuma ki haifi 'da. Za ki ba shi suna Yesu. Zai zama 'Dan Madaukaki Allah zai kuma yi mulki har abada."

Maryamu ta amsa, "Yaya wannan zai kasance da shike ni budurwa ce?" Mala'ikan yayi bayyani, "Ruhu Mai Tsarki zai zo gare ki, ikon Allah kuma zai lullube ki. Ta haka jaririn zai zama mai tsarki, 'Dan Allah." Maryamu ta gaskanta ta kuma amince da abinda Mala'kan ya fada.

Ba da jimawa ba bayan mala'ikan yayi magana da Maryamu, sai ta tafi ta ziyarci Alisabatu. Da jin muryar gaisuwar Maryamu, sai jaririn Alisabatu yayi tsalle a cikinta. Matan suka yi murna tare game da abinda Allah ya riga yayi dominsu. Bayan wata uku da Maryamu ta ziyarci Alisabatu, Maryamu ta koma gida.

Bayan Alisabatu ta haifi danta namaiji, Zakariya da Alisabatu suka ba jaririn suna Yahaya, kamar yadda mala'ika ya umarta. Sai Allah ya yarda wa Zakariya yayi magana kuma. Zakariya yace, "Yabo ga Allah, domin ya tuna da mutanensa! Kai, da na, za a kira ka annabin Madaukaki Allah wanda zai gaya wa mutane yadda zasu karbi gafara domin zunubansu!''

Informations reliées

Mots de Vie - GRN présente des messages sonores évangéliques dans des milliers de langues à propos du salut et de la vie chrétienne.

Téléchargements gratuits - Ici vous allez trouver le texte pour les principaux messages GRN en plusieurs langues, plus des images et autres documents prêts à télécharger

La collection d'Enregistrements de GRN - Matériel d'évangélisation et d'enseignement biblique de base adapté aux besoins et à la culture du peuple, dans une variété de styles et de formats.

Copyright and Licensing - GRN shares it's audio, video and written scripts under Creative Commons

Choosing the right audio or video format - What audio and video file formats are available from GRN, and which one is best to use?