unfoldingWord 25 - Shaidan ya jarabci Yesu
Pääpiirteet: Matthew 4:1-11; Mark 1:12-13; Luke 4:1-13
Käsikirjoituksen numero: 1225
Kieli: Hausa
Yleisö: General
Genre: Bible Stories & Teac
Hienostuneisuutta: General
Tarkoitus: Evangelism; Teaching
Raamatun lainaus: Paraphrase
Tila: Approved
Käsikirjoitukset ovat perusohjeita muille kielille kääntämiseen ja tallentamiseen. Niitä tulee mukauttaa tarpeen mukaan, jotta ne olisivat ymmärrettäviä ja merkityksellisiä kullekin kulttuurille ja kielelle. Jotkut käytetyt termit ja käsitteet saattavat vaatia lisäselvitystä tai jopa korvata tai jättää kokonaan pois.
Käsikirjoitusteksti
Nan da nan bayan an yi wa Yesu baftisma, Ruhu Mai Tsarki ya bishe Yesu zuwa jeji, in da ya yi azumi kwanaki da dare arba'in, sai Shaidan ya zo wurin Yesu ya jarabce shi domin ya yi zunubi.
Shaidan ya jarabci Yesu yana cewa, in kai ne dan Allah, ka mai da duwatsun nan gurasa, don ka ci
Yesu amsa ya ce, "A rubuce ya ke a kalmar Allah, 'Mutane basu bukatar gurasa kawai don su rayu, amma suna bukatar kowace kalma da Allah yake fada!"'
Sa'annan Shaidan ya dauki Yesu ya kai shi saman haikali a wurin da ya fi tsawo duka, ya ce masa, "In kai ne dan Allah ka yi tsalle daga nan zuwa kasa, domin a rubuce yake, 'Allah zai umurci mala'ikunsa su tallafe ka domin kada kafanka ya yi tuntube da dutse.'''
Amma Yesu ya amsa wa Shaidan da abinda aka rubuta daga cikin Nassi. Ya ce, "A kalmar Allah, ya umurci mutanensa, 'Kada ku gwada Ubangiji Allahn ku."'
Sai Shaidan ya nuna wa Yesu dukkan mulkokin duniya da dukkan daukakarsu kuma ya ce, "Zan baka dukkan wannan, idan ka rusuna ka yi mani sujada."
Yesu amsa "Rabu da ni, shaidan! A kalmar Allah ya umurci mutanensa, 'Ku yi wa Ubangiji Allahn ku sujada shi kadai kuma za ku bauta wa"'
Yesu bai fada cikin jerabobin Shaidan ba, saboda haka Shaidan ya rabu da shi. Sai mala'iku suka zo suka yi wa Yesu hidima.