unfoldingWord 11 - Ketarewa
Pääpiirteet: Exodus 11:1-12:32
Käsikirjoituksen numero: 1211
Kieli: Hausa
Yleisö: General
Genre: Bible Stories & Teac
Tarkoitus: Evangelism; Teaching
Raamatun lainaus: Paraphrase
Tila: Approved
Käsikirjoitukset ovat perusohjeita muille kielille kääntämiseen ja tallentamiseen. Niitä tulee mukauttaa tarpeen mukaan, jotta ne olisivat ymmärrettäviä ja merkityksellisiä kullekin kulttuurille ja kielelle. Jotkut käytetyt termit ja käsitteet saattavat vaatia lisäselvitystä tai jopa korvata tai jättää kokonaan pois.
Käsikirjoitusteksti
Allah ya gargadi Fir'auna, cewa idan bai saki yayan Isra'ila su tafi ba, zai kashe dukan yan fari maza na mutane Masar da dabbobi. Da Fir'auna ya ji wannan, har yanzu ya ki ya gaskanta ya kuma yi biyaya da Allah.
Allah yayi tanadin hanyar ceton dan farin duk wanda ya gaskanta ga shi. Kowace iyali ta zabi dan rago mara lahani ta yanka
Allah ya fada wa Isra'ilawa su shafa jinin dan ragon kewaye da kofar gidansu, su gasa nama su ci agagauce tare da gurasa mara yisti. Ya kuma fada masu su shirya su bar Masar bayan sun ci
Israilawa sun yi komai kamar yadda Allah ya umurce su su yi. Da tsakar dare, Allah ya ratsa cikin Masar ya na kishan kowane dan fari.
Dukan gidajen Israilawa na shafe da jini kewaye da kofofin su, Allah ya ketare gidajen. Kowa da ke cikin su ya tsira. Sun tsira saboda jinin dan ragon
Amma Masarawa basu gaskanta Allah ko su yi biyaya da umuninsa ba. Don haka Allah bai ketare gidajensu ba, Allah ya kashe kowane daya na yayan fari maza na Masarawa.
Kowane dan fari na Masar ya mutu, daga dan farin wanda yake daure a kurkuku, zuwa dan farin Fir'auna. mutane da dama a Masar sun yi kuka da kururuwa saboda tsananin bakin ciki.
A wannan daren, Fir;auna ya kira Musa da Haruna ya ce, "Dauki Israilawa ku bar Masar nan take!" Mutanen Masar kwa suka roki Isra'ilawa su tafi nan take.