Valige keel

mic

Jaga

Jaga linki

QR code for https://globalrecordings.net/script/ha/1240

unfoldingWord 40 - An Gicciye Yesu

unfoldingWord 40 - An Gicciye Yesu

Kontuur: Matthew 27:27-61; Mark 15:16-47; Luke 23:26-56; John 19:17-42

Skripti number: 1240

Keel: Hausa

Publik: General

Eesmärk: Evangelism; Teaching

Features: Bible Stories; Paraphrase Scripture

Olek: Approved

Skriptid on põhijuhised teistesse keeltesse tõlkimisel ja salvestamisel. Neid tuleks vastavalt vajadusele kohandada, et need oleksid arusaadavad ja asjakohased iga erineva kultuuri ja keele jaoks. Mõned kasutatud terminid ja mõisted võivad vajada rohkem selgitusi või isegi asendada või täielikult välja jätta.

Skripti tekst

Bayan sojojin sun yi wa Yesu ba'a, sai suka tafi da shi domin su gicciye shi. Suka sa shi ya dauki gicciyen da zai mutu akai.

Sojojin suka kawo Yesu wurin da ake kira, "Kokon kai" suka kafe hannayensa da kafafunsa da kusa akan gicciye. Amma Yesu ya ce, "Uba ka gafarta masu domin basu san abin da suke yi ba." Bilatus ya bada umarni su rubuta, "Sarkin Yahudawa" akan allo su kuma sa shi akan gicciyen, sama da kan Yesu.

Sojojin suka yi kuri'a akan tufafin Yesu. Sa'anda suka yi haka, sun cika wani annabci da ya ce, "Sun raba tufafina a tsakaninsu, suka sa kuri'a akan tufa ta."

Aka gicciye Yesu tsakanin 'yan fashi biyu. Daya daga cikinsu ya yi wa Yesu ba'a, amma dayan ya ce, "Baka da tsoron Allah? mu mun yi laifi amma wannan mutumin bashi da laifi." Sa'anan ya ce wa Yesu, "In ka yarda ka tuna da ni a mulkinka." Yesu ya amsa masa. "Yau zaka kasance tare da ni a fiddausi."

Shugbannin Yahudawa da wadansu mutane a cikin taron suka yi wa Yesu ba'a. Suka ce masa, "Idan kai 'Dan Allah ne sauko daga kan gicciyen ka ceci kanka! sa'annan zamu gaskanta ka."

Sai sararin sama na lardin ya yi baki gaba daya, ko da yake da tsakiyar rana ne. Wuri ya zama duhu da tsakar rana, aka kuma ci gaba da duhu har sa'a uku.

Sa'anan Yesu yi kuka, "Ya kare! Uba na bada ruhu na a cikin hannun ka." Sai ya sunkuyar da kansa ya saki ruhunsa. Da ya mutu an yi girgizar kasa, sai babban labulen da ya raba mutane da Allah a Haikali, ya tsage biyu, daga sama zuwa kasa.

Ta wurin mutuwarsa, Yesu ya bude hanya da mutane za su zo gun Allah. Da sojan nan mai tsaron Yesu ya ga dukkan abubuwan da suka faru, sai ya ce, "Hakika, wannan mutumin marar laifi ne. Shi Dan Allah ne."

Sa'annan Yusufu da NIkodimas, shugabannin Yahudawa biyu wadanda suka gaskanta, Yesu Almasihu ne, suka tambayi Bilatus jikin Yesu. Suka nade jikinsa cikin zani suka sa shi cikin kabarin dutse da aka sassaka. Sa'anan suka mirgina babban dutse a bakin kabarin domin su rufe kofar.

Seotud Informatsioon

Elu Sõnad - Piiblil põhinevad sõnumid päästmise ja kristliku elu kohta tuhandetes keeltes evangeeliumi helisalvestistes.

Copyright and Licensing - GRN shares its audio, video and written scripts under Creative Commons

Choosing the audio or video format to download - What audio and video file formats are available from GRN, and which one is best to use?