unfoldingWord 49 - Sabuwar Alkawarin Allah

unfoldingWord 49 - Sabuwar Alkawarin Allah

Outline: Genesis 3; Matthew 13-14; Mark 10:17-31; Luke 2; 10:25-37; 15; John 3:16; Romans 3:21-26, 5:1-11; 2 Corinthians 5:17-21; Colossians 1:13-14; 1 John 1:5-10

Script Number: 1249

Language: Hausa

Audience: General

Genre: Bible Stories & Teac

Purpose: Evangelism; Teaching

Bible Quotation: Paraphrase

Status: Approved

Scripts are basic guidelines for translation and recording into other languages. They should be adapted as necessary to make them understandable and relevant for each different culture and language. Some terms and concepts used may need more explanation or even be replaced or omitted completely.

Script Text

Wani mala'ika ya ce wa wata budurwa wanda ake ce da ita Maryamu, zata haifi Dan Allah.Tun tana budurwa Ruhu Mai Tsarki ya lullube ta, ta kuma yi ciki. Ta haifi da ta kuma sa masa suna Yesu. Domin haka, Yesu Allah ne kuma mutum.

Yesu yayi al'ajibai da yawa da suka bada tabbatarwa shi Allah ne. Yayi tafiya akan ruwa, ya lafar da ruwan sama mai iska, ya warkar da mutane marasa lafiya da yawa, ya kori aljannu, ya tada matattu zuwa rai, ya juya dunkulen gurasa biyar da kifi biyu zuwa issashen abinci domin mutane fiye da 5,000.

Yesu kuma babban mallami ne, ya kuma yi magana da iko saboda shi Dan Allah ne. Ya koyar cewa, ya kamata ka kaunaci sauran mutane kamar yadda kake kaunar kanka.

Ya kuma koyar cewa, ya kamata ka kaunaci Allah fiya da yadda zaka kaunaci sauran abubuwa, harma da dukiyar ka.

Yesu yace, mulkin Allah yafi komai a duniya daraja. Abu mafi muhimmanci ga kowa shine ya kasance a mulkin Allah. Idan zaka shiga mulkin Allah, dole ne a cece ka daga zunuban ka.

Yesu ya koyar cewa wadansu mutane zasu karbe shi su kuma sami ceto, amma wadansu ba zasu karba ba. Ya ce wadansu mutane suna kama da kasa mai kyau. Sun karbi labari mai dadi na Yesu kuma suka sami ceto. Wadansu mutane suna kama da kasa mai tauri dake kan hanya, inda irin maganar Allah ba ya shiga, kuma basa ba da wani amfani. Wadannan mutanen sukan ki sako game da Yesu kuma baza su shiga mulkinsa ba.

Yesu ya koyar da cewa, Allah yana kaunar masu zunubi kwarai. Yana so ya gafarta masu, ya kuma maishe su 'ya'yansa.

Yesu kuma ya gaya mana ce wa Allah ya tsani zunubi. Sa'anda da Adamu da Hauwa'u suka yi zunubi, ya shafi dukkan zuriyar su. Sakamakon haka, kowane mutum a duniya ya yi zunubi, a rabe kuma ya ke da Allah. Domin haka, kowa ya zama abokin gaba na Allah.

Amma Allah ya kaunaci kowa a duniya sosai harma ya bada makadaicin dansa, domin duk wanda ya ba da gaskiya ga Yesu ba za a hukunta shi saboda zunubansa ba, amma zai kasance tare da Allah har abada.

Saboda zunubinka, kayi laifi kuma ka cancanci mutuwa. Ya kamata Allah yayi fushi da kai, amma ya zuba fushinsa akan Yesu amaimakonka. Sa'adda Yesu ya mutu akan giciye, ya karbi hukuncinka.

Yesu bai taba yin zunubi ba, amma ya zabi a hukuntashi, kuma ya mutu a matsayin hadaya cikakkiya domin ya kawar da zunubanka da zunuban kowanne mutum a duniya. Saboda Yesu ya mika kansa hadaya, Allah zai iya gafarta kowanne zunubi, har ma da munanan zunubai.

Ayyuka nagari ba zasu cece ka ba, Babu abinda za ka iya yi ka sami dangantaka da Allah. Yesu ne kadai zai iya wanke zunubanka. Dole ne ka gaskanta Yesu Dan Allah ne, ya kuma mutu akan gicciye maimakon ka, Allah ya kuma tashe shi da rai.

Allah zai cece duk wanda ya bada gaskiya ga Yesu, ya kuma karbe shi a matsayin Ubangijinsu. Amma ba zai ceci ko dayan da bai ba da gaskiya gare shi ba. Ba ya zabi ko kai mai arzikine ko talaka, na miji ko ta mace, tsoho ko matashi, ko inda kake zama. Allah yana kaunar ka kuma yana so ka bada gaskiya ga Yesu domin ya sami dangantaka na kusa da kusa.

Yesu na gaiyatarka ka bada gaskiya gare shi kuma ayi maka baftisma. Ka bada gaskiya Yesu shine Almasihu, makadaicin Dan Allah? Ka bada gaskiya kai mai zunubi ne kuma ka cancanci Allah ya hukunta ka? Ka gaskanta Yesu ya mutu akan gicciye domin ya dauke zunubanka?

Idan ka bada gaskiya ga Yesu da abinda yayi maka, kai Krista ne! Allah ya fitar da kai daga mulkin Shaidan ta duhu, kuma ya saka cikin Mulkin Allah na haske. Allah ya dauke tsofofin hanyoyin yin zunubin ka, ya kuma baka sabobin hanyoyin yin adalci.

Idan kai Kirista ne, Allah ya gafarta zunubanka saboda abinda Yesu ya yi. Yanzu, Allah na ganin ka a matsayin abokin sa na kusa a maimakon makiyi.

Idan kai abokin Allah ne da kuma bawan Yesu Ubangiji, za ka so kayi biyayya da abinda Yesu yake koya maka. Ko da shike kai Krista ne, za'a iya jarabtar ka yi zunubi. Amma Allah mai aminci ne kuma yace idan ka furta zunubanka, zai yafe maka. Zai baka karfi kayi yaki da zunubi.

Allah yace kayi addu'a, kayi nazarin maganarsa, ka bauta masa tare da sauran Kiristoci, ka kuma gaya wa wadansu abinda ya yi maka. Dukkan wadannan abubuwa za su taimake ka wurin samun dangantaka mai zurfi da shi.

Related information

Words of Life - Audio gospel messages in thousands of languages containing Bible based messages about salvation and Christian living.

Free downloads - Here you can find all the main GRN message scripts in several languages, plus pictures and other related materials, available for download.

The GRN Audio Library - Evangelistic and basic Bible teaching material appropriate to the people's need and culture in a variety of styles and formats.

Copyright and Licensing - GRN shares it's audio, video and written scripts under Creative Commons

Choosing the right audio or video format - What audio and video file formats are available from GRN, and which one is best to use?