unfoldingWord 14 - Yawo acikin Jeji

unfoldingWord 14 - Yawo acikin Jeji

Outline: Exodus 16-17; Numbers 10-14; 20; 27; Deuteronomy 34

Script Number: 1214

Language: Hausa

Audience: General

Genre: Bible Stories & Teac

Purpose: Evangelism; Teaching

Bible Quotation: Paraphrase

Status: Approved

Scripts are basic guidelines for translation and recording into other languages. They should be adapted as necessary to make them understandable and relevant for each different culture and language. Some terms and concepts used may need more explanation or even be replaced or omitted completely.

Script Text

Bayanda Allah ya fada wa isra'ilawa dokokin da yake so su yi biyayya da su a matsayin alkawarin sa da su, suka tafi daga dutsen Sina'i. Allah ya fara jagorar su zuwa yankin kasar alkawari, wanda kuma ake kira kan'ana. Al'amudin girgije na tafiye a gabansu zuwa kan'ana su kuma suna biye da shi.

Allah yayi wa Ibrahim, Ishaku, da Yakubu alkawari cewa zai bada kasar alkawari ga zuri'ar su, amma yanzu akwai kungiyoyin mutane da yawa dake zaune a wurin. Ana kiran su kan'aniwa. Kan'aniwa basu bauta ko su yi biyayya da Allah ba. Suna bautar allolin karya kuma suna yin miyagun abubuwa da yawa.

Allah ya cewa Isra'ilawa, "Lalle ne ku kawar da dukkan Kan'aniwa acikin kasar alkawari. Kada ku yi yarjejjeniyar salama da su kuma kada ku aure su. Lelle ne ku hallakar da dukkan gumakunsu gabaki daya. Idan ba ku yi biyayya da ni ba, zaku bauta ma gumakunsu a maimako na."

Sa'anda Isra'ilawa suka iso gabar Kan'ana, Musa ya zabi mutum goma sha biyu, daya daga kowace kabilar Isra'ila. Ya basu umurni su je lekan asirin kasar su kuma gani yadda ta ke. Su kuma dubi yanayin Kan'aniwa su gani ko suna da karfi ko kasassu.

Mutanen nan goma sha biyu suka yi tafiya cikin Kan'ana kwana arba'in sa'an nan suka komo. Suka fada wa jama'ar, "Kasar na da albarka kuma ga yawan anfani!" Amma goma daga cikin masu lekan asirin suka ce, "Birnin na da karfin gaske kuma mutanen katti ne! Idan muka kai masu hari, tabbas zasu fi karfin mu kuma su kashe mu!"

Nan take Kalibu da Joshua, biyu daga cikin masu lekan asirin, suka ce, "Gaskiya ne mutanen Kan'ana dogi ne kuma karfafa, amma tabbas za mu sha karfin su, Allah zai yi yaki amadadin mu!"

Amma mutanen basu saurari Kalibu da Joshua ba. Suka yi fushi da Musa da Haruna suna cewa, "Me yasa kuka kawo mu wannan mummunar wuri? Da ma mun zauna a Masar maimakon a kashe mu cikin yaki kuma a maida matanmu da yayan mu bayi." Mutanen suna so su zabi wani shugaba dabam wanda zai komar da su Masar.

Allah ya husata kwarai har ma ya zo alfarwar saduwa. Allah yace, "Domin kunyi tawaye agare ni, dukkan mutane zasu yi famar yawo a daji. Banda Joshua da Kalibu, kowane daya dake shekara ashirin ko fiye zai mutu acan kuma ba zai taba shiga kasar alkawarin ba."

Da mutanen suka ji haka, suka tuba don sunyi zunubi. Suka dauki kayan yakinsu suka tafi domin su yaki mutanen Kan'ana. Musa kuwa ya gargade su kada su je domin Allah baya tare da su, amma basu saurare shi ba.

Allah bai tafi tare da su zuwa yakin ba, saboda haka aka yi nasara akan su kuma aka kashe da yawa acikin su. Sa'annan Isra'ilawa suka juya wa Kan'ana baya kuma su ka yi faman yawo a daji har shekaru arba'in.

Cikin shekaru arba'in da mutanen Isra'ila suka yi suna yawo a daji, Allah yana yi masu tanadi. Allah ya basu gurasa daga sama, da ake kira "Manna." Ya kuma aiko da yan tsalwa (wanda suke kananan tsuntsaye) a cikin taronsu domin su sami nama su ci. Cikin dukkan lokacin nan, Allah ya kare kayakinsu da takalmansu daga kodewa.

Allah kuwa cikin al'ajibinsa ya basu ruwa daga dutse. Amma duk da haka, mutanen Isra'ila suka yi gunaguni game da Allah da Musa. Duk da haka, adalcin Allah bisa alkawarinsa ga Ibrahim, da Ishaku da Yakubu bai sake ba.

Wani lokaci sa'adda mutanen suka rasa ruwa, Allah ya ce wa Musa, "Yi magana da dutse, ruwa kuwa zai fito daga ita." Amma Musa bai girmama Allah agaban dukkan mutanen ba ta wurin buga dutsen sau biyu da sanda amaimakon magana da ita. Ruwa kuwa ya fito daga dutsen domin kowa ya sha, amma Allah yana fushi da Musa kuma yace, "Bazaka shiga kasar alkawarin ba."

Bayan da Isra'ilawa suka yi ta zagaya acikin daji har shekaru arba'in, dukkan wadanda suka yi tawaye ga Allah sun mutu. Sa'annan Allah ya jagoranci mutanen zuwa iyakar kasar alkawari kuma. Musa kuwa ya tsufa sosai, sai Allah ya zabi Joshua ya taimake shi da shugabantar mutanen. Allah kuwa yayi wa Musa alkawari da cewa wata rana, zai aiko da wani annabi kamar Musa.

Sa'annan Allah ya ce wa Musa ya haura saman dutsen domin ya kalli kasar alkawarin. Musa kuwa ya kalla kasar alkawarin amma Allah bai yarda masa ya shiga ba. Sa'annan Musa ya mutu, Isra'ilawa kuwa suka yi makokinsa har kwana talatin. Joshua kuwa ya zama sabon shugabansu. Joshua shugaba ne nagari domin ya dogara kuma yana biyayya ga Allah.

Related information

Words of Life - Audio gospel messages in thousands of languages containing Bible based messages about salvation and Christian living.

Free downloads - Here you can find all the main GRN message scripts in several languages, plus pictures and other related materials, available for download.

The GRN Audio Library - Evangelistic and basic Bible teaching material appropriate to the people's need and culture in a variety of styles and formats.

Choosing the audio or video format to download - What audio and video file formats are available from GRN, and which one is best to use?

Copyright and Licensing - GRN shares it's audio, video and written scripts under Creative Commons