unfoldingWord 13 - Alkawarin Allah da Isra'ila

unfoldingWord 13 - Alkawarin Allah da Isra'ila

Outline: Exodus 19-34

Script Number: 1213

Language: Hausa

Audience: General

Genre: Bible Stories & Teac

Purpose: Evangelism; Teaching

Bible Quotation: Paraphrase

Status: Approved

Scripts are basic guidelines for translation and recording into other languages. They should be adapted as necessary to make them understandable and relevant for each different culture and language. Some terms and concepts used may need more explanation or even be replaced or omitted completely.

Script Text

Bayan da Allah ya jagoranci Isra'ilawa suka ratsa Jan Teku, Ya jagorance su cikin daji zuwa dutsen da ake kira Sinai. Wannan shine dutsen da Musa ya gani daji na konewa da wuta. Mutanen kuwa suka gina alfarwa a karkashin dutsen.

Allah ya ce wa Musa da kuma jama'ar Isra'ila, "Idan za kuyi biyayya da ni ku kuma kiyaye alkawarina, za ku zama mallaka ta mai tamani, rundunan firistoci, kuma al'umma mai tsarki."

Bayan kwanaki uku, bayan da mutanen suka shirya kansu da ruhaniyarsu, Allah ya sauko a kan dutsen sina'i da aradu, da walkiya, da hayaki da busar kaho mai kara. Musa ne kadai aka yarda ya haura kan dutsen.

Sa'annan Allah ya basu alkawarin, ya ce, "Ni ne Yahweh, Allahn ku, wanda ya cece ku daga bauta a Masar. Kada ku bauta wa wassu alloli."

"Kada ku kera gumaka kuma kada ku bauta masu, domin Ni, Yahweh, Allah mai kishi ne. Kada ku yi anfani da sunana a rainannun al'amura. Ku tabbata kun kebe ranar asabar da tsarki. Saboda haka, ku yi dukkan ayyukanku a kwanaki shida, domin rana ta bakwai ranar hutu ce agare ku da kuma na tunawa da ni."

"Ka girmama mahaifin ka da mahaifiyar ka. Kada ka yi kisa. Kada ka yi zina. Kada ka yi sata. Kada ka yi karya. Kada ka yi sha'awar matar makwabcin ka, gidan sa, ko wani abinda ke mallakarsa."

Sa'annan Allah ya rubuta wadannan dokoki goma akan Alluna guda biyu kuma ya baiwa Musa. Allah kuma ya bada shari'u da dama da kuma ka'idodi da za'a bi. Idan mutane sunyi biyayya da wadannan shari'u, Allah yayi alkawari cewa zai albarkace su ya kuma kare su. Idan suka ki yin biyayya da su kuma Allah zai hukunta su.

Allah ya sake baiwa Isra'ilawa cikakken kwatancin alfarwa da yake so su kera. Ana kiran ta alfarwar saduwa, kuma yana da dakuna biyu, arabe da baban labule. Babban firist ne kadai ke da iznin shiga dakin da ke bayan labulen, domin Allah na kasancewa awurin.

Duk wanda bai yi biyayya da shari'ar Allah ba zai kawo dabba a bagadi dake gaban alfarwa ta saduwa domin hadaya ga Allah. Firist zai yanka dabbar ya kona a kan bagadi. Jinin dabbar da aka yi hadayan zai rufe zunubin mutumin kuma ya tsarkake mutumin a gaban Allah. Allah ya zabi dan'wan Musa, Haruna, da zuriyar Haruna su zama firistocin sa.

Dukkan jama'a suka amince su yi biyayya da Shari'a da Allah ya basu, su bauta wa Allah shi kadai, su kuma kasance mutanensa na musamman. Amma nan bada jimawa ba bayan da suka yi alkawarin yin biyayya ga Allah, sai suka yi mummunar zunubi.

Kwanaki da dama, Musa yana kan dutsen Sina'i yana magana da Allah. Mutanen kuwa suka gaji da jiran dawowarsa. Sai suka kawo ma Haruna zinariya suka roke shi ya kera masu gumaka!

Haruna ya yi gunkin zinariya mai sifar maraki. Mutanen suka fara bautan gumakan suna mika hadayu ga ita! Allah ya husata dasu kwarai domin zunubin su ya kuwa yi shirin hallaka su. Amma Musa yayi addu'a domin su, Allah ya ji addu'ar sa kuma bai hallaka su ba.

Bayanda Musa ya sauko daga dutsen ya ga gunkin, ya husata kwarai har ma ya murguje allunan nan da Allah ya rubuta dokoki goma akai.

Sa'annan Musa ya daka gunkin ya zama gari, ya zuba garin acikin ruwa kuma ya sa mutanen suka sha ruwan. Allah ya aiko da annuba ga mutanen kuma da yawa suka mutu.

Musa ya kera sabon alluna domin dokoki goma maimakon wadanda suka murguje. Sa'annan ya sake haurawa dutsen kuma yayi addu'a Allah ya gafarta wa mutanen. Allah ya saurari Musa ya kuwa gafarta masu. Musa ya sauko daga kan dutsen da sabon alluna dauke da dokoki goma. Sai Allah ya jagoranci isra'ilawa daga dutsen sina'i zuwa yankin kasar alkawari.

Related information

Words of Life - Audio gospel messages in thousands of languages containing Bible based messages about salvation and Christian living.

Free downloads - Here you can find all the main GRN message scripts in several languages, plus pictures and other related materials, available for download.

The GRN Audio Library - Evangelistic and basic Bible teaching material appropriate to the people's need and culture in a variety of styles and formats.

Choosing the audio or video format to download - What audio and video file formats are available from GRN, and which one is best to use?

Copyright and Licensing - GRN shares it's audio, video and written scripts under Creative Commons