unfoldingWord 12 - Fitowa

unfoldingWord 12 - Fitowa

Outline: Exodus 12:33-15:21

Script Number: 1212

Language: Hausa

Audience: General

Genre: Bible Stories & Teac

Purpose: Evangelism; Teaching

Bible Quotation: Paraphrase

Status: Approved

Scripts are basic guidelines for translation and recording into other languages. They should be adapted as necessary to make them understandable and relevant for each different culture and language. Some terms and concepts used may need more explanation or even be replaced or omitted completely.

Script Text

Isra'ilawa sun yi farin cikin barin Masar, sun fita daga bauta, sun kama hanya zuwa kasar alkawari! Masarawa sun ba su duk abin da suka tambaye su, har zinari, azurfa da kaya masu muhimminci, wadansu daga alummai sun gaskata da Allah, suka bi Isra'ilawa sa'anda suka fita daga Masar.

Allah ya bishe su da al'amudin girgije da ke gaban su da rana, wanda ya ke zama al'amudin wuta da dare. Allah yana tare da su kuma yana shiryar da su kowane lokaci sa'anda suke tafiya. Duk abinda za su yi shine su bi shi.

Bayan dan lokaci, Fir'auna da mutanensa suka chanza ra'ayi, sun nemi Isra'ilawa su dawo bauta kuma. Allah ya sa Fir'auna ya taurara zuciyarsa domin dukkan mutane su san cewa shi, Yahweh, shine Allah na gaske, Ikon sa kuma ya sha karfin Fir'auna da allolinsa.

Saboda haka Fir'auna da mayakansa suka bi Isra'ilawa su maishe su bayin su kuma. Da Isra'ilawa sun gan mayakan Masarawa na zuwa, sai suka gane cewa sun fada tarko tsakanin mayakan Msarawa da jan teku. Sai suka tsorata sosai, suka yi kuka, "Me ya sa muka bar Masar? Zamu mutu!"

Musa ya ce wa Isra'ilawa, "Ku bar jin tsoro! Allah zai yi yaki domin ku yau kuma zai cece ku." Sai Allah ya ce wa Musa, "Ka gaya wa Isra'ilawa su yi gaba su nufi jan tekun."

Sai Allah ya matsar da al'amudin girgije ya saka shi tsakanin Isra'ilawa da Masarawa, Masarawa suka kasa ganin Isara'ilawa.

Allah ya ce wa musa ka daga hannunka bisa tekun ka raba ruwayen, sai Allah ya sa iska ta raba tekun zuwa hagu da dama, sai hanya ta kasance a tsakiyan tekun.

Isra'ilawa suka wuce a busassar kasa a tsakiyan tekun da bagon ruwa a kowace gefe.

Allah ya daga al'amudin girgije sama domin Masarawa suka gan Isra'ilawa na tserewa. Sai Masarawa suka yanke shawara su bi su.

Sai suka bi Isra'ilawa akan hanyan da ya ratsa tekun, amma Allah ya sa Masarawa suka tsorata ya kuma sa karusansu sun makalewa. Sai suka yi ihu, "Mu gudu! Allah na yi wa Isra'ilawa yaki!"

Bayan dukkan Isra'ilawa sun ketare zuwa dayan gefen tuken lafiya, Allah ya ce wa Musa sake mika hannun ka. Da ya yi biyayya, sai ruwan tekun ya rufe mayakan Masarawa, ya koma wurinsa kamar da. Dukkan mayakan Masarawa suka nutse.

Sa'anda Isra'ilawa sun gan cewa Masarawa sun mutu, sai suka dogara ga Allah kuma suka gaskanta cewa Musa annabin Allah ne.

Isra'ilawa sun yi murna da farin ciki sosai domin Allah ya cece su daga mutuwa da bauta! Yanzu sun sami yanci su bauta wa Allah. Isra'ilawa suka yi wakoki masu yawa, suna bukin samun sabuwar yancin su, sun yi yabon Allah domin ya cece su daga mayakan Masarawa.

Allah ya umurci Isra'ilawa su yi bukin idin ketarewa a kowace shekara domin tunawa da nasara da ya basu bisa Masarawa da kuma ceton su daga bauta. Sun yi bukin tawurin yanka dan rago marar lahani, da cin gurasa mara yeast.

Related information

Words of Life - Audio gospel messages in thousands of languages containing Bible based messages about salvation and Christian living.

Free downloads - Here you can find all the main GRN message scripts in several languages, plus pictures and other related materials, available for download.

The GRN Audio Library - Evangelistic and basic Bible teaching material appropriate to the people's need and culture in a variety of styles and formats.

Copyright and Licensing - GRN shares it's audio, video and written scripts under Creative Commons

Choosing the right audio or video format - What audio and video file formats are available from GRN, and which one is best to use?