unfoldingWord 03 - Ruwan Tufana

unfoldingWord 03 - Ruwan Tufana

Outline: Genesis 6-8

Script Number: 1203

Language: Hausa

Theme: Eternal life (Salvation); Living as a Christian (Obedience); Sin and Satan (Judgement)

Audience: General

Genre: Bible Stories & Teac

Purpose: Evangelism; Teaching

Bible Quotation: Paraphrase

Status: Approved

Scripts are basic guidelines for translation and recording into other languages. They should be adapted as necessary to make them understandable and relevant for each different culture and language. Some terms and concepts used may need more explanation or even be replaced or omitted completely.

Script Text

Bayan tsawon lokaci, mutane da yawa suna rayuwa a cikin duniya. Suka zama mugaye masu husuma. Wannan kuwa yayi muni matuka, har Allah ya yanki shawara ya hallakar da dukkan duniya da gagarumar ambaliya.

Amma Nuhu ya sami tagomashi a wurin Allah. Shi mutum ne mai adalci, yana kuma zama cikin mugayen mutane. Allah ya gaya wa Nuhu game da ruwan tufanar da yake shirin aikowa. Ya gaya wa Nuhu ya gina babban jirgin ruwa.

Allah kuma ya gaya wa Nuhu ya gina jirgin da misalin tsawo kamu 140, fadi 23, tsayi kuma 13.5. Nuhu zai gina jirgin da katako, hawa uku da kuma dakuna ma su yawa, soro da kuma taga. Jirgin kuma zai dauki Nuhu da iyalinsa, da ko wane irin dabba dake fuskar kasa, sa'adda za'a yi ruwan tufana.

Nuhu ya yi biyayya da Allah. Shi da 'ya'yan sa uku suka gina jirgin kamar yadda Allah ya fada masu. Ginin jirgin kuwa ya dauki shakaru da yawa, saboda da girma sa. Nuhu kuma ya gargadi mutune game da ruwan tufana da ke zuwa, ya gaya masu su juyo ga Allah, amma basu gasganta shi ba.

Allah kuma ya umarci Nuhu da iyalinsa su yi tanadin abincin da zai ishe su, da kuma dabbobi. Sa'anda aka gama kome, sai Allah ya ce wa Nuhu lokaci yayi da shi, da matarsa, da 'ya'yansa uku da matan su, zasu shiga jirgin, mutane takwas kenan gaba daya.

Allah ya aiko namiji da tamace na kowane irin dabba da kuma tsutsu, wurin Nuhu domin su shiga jirgin su tsira lokacin da za'ayi ruwan tufana. Allah ya aiko maza bakwai da mata bakwai na kowane irin dabba da za'a iya amfani da su domin hadaya. Sa'adda dukka suka shiga jirgin, Sai Allah ya rufe kofar jirgin da kansa.

Sai aka fara ruwan sama, aka yi ta ruwa, aka yi ta ruwa. Aka yi ruwa yini arba'in da dare arba'in ba tsayawa! Ruwa kuma ya rika bubbugowa daga kasa a duniya. Ruwa kuma ya rufe kome dake cikin dukkan duniya, harma da tsaunuka da suka fi tsayi.

Dukkan abinda ke da rai a kan busasshiyar kasa ya mutu, saidai mutane da dabbobin dake cikin jirgin. Jirgin kuwa ya rika reto a kan ruwa, ya kuma tsirar da dukkan abinda ke cikinsa daga nutsewa.

Bayan da ruwan ya tsaya, jirgin yayi ta reto bisa ruwa na wata biyar, kuma a wannan lokacin ne ruwan ya fara janyewa. Watarana sai jirgin ya tsaya a kan wani dutse, amma duniya har yanzu tana mamaye da ruwa. Bayan karin watanni uku, sai saman tsaunuka suka bayyana.

Bayan karin kwana arba'in, sai Nuhu ya aiki tsuntsuwar da ake kira hankaka, domin ta ga ko ruwan ya janye. Amma hankakar ta yi ta firiya tana neman busashiyar kasa, ba ta samu ba.

Bayan haka Nuhu ya aiki tsuntsuwa da ake kira kurciya, ita ma bata sami busasshiyar kasa ba, sai ta dawo wurin Nuhu. Bayan mako guda ya sake aikan kurciyar, sai ta dawo da ganyen zaitun a bakinta! Ruwa ya fara janyewa, tsire-tsire kuma sun fara girma!

Nuhu ya sake jira mako guda sa'annan ya sake aikan kurciyar a karo na uku. A wannan lokacin kuwa ta sami wurin sauka, bata sake dawowa ba. Ruwan yana bushewa!

Bayan watanni biyu Allah ya ce wa Nuhu, ''Da kai da iyalinka da dukkan dabbobi zaku iya fita daga cikin jirgin yanzu. Ku haifi 'ya'ya da yawa da jikoki, ku kuma cika duniya.'' Sai Nuhu da iyalinsa suka fita daga jirgin.

Bayan Nuhu ya fita daga jirgin sai ya gina bagade, ya kuma yi hadaya da wassu daga cikin ire iren dabbobin da za'a iya yin hadaya da su. Allah kuma ya yi farinciki da hadayar, ya albarkaci Nuhu da iyalinsa.

Allah ya ce, ''Na yi alkawari ba zan sake la'anta kasa saboda miyagun ayyukan da mutane ke yi ba, ko in hallaka duniya ta wurin ruwan tufana, kodashike mutane masu zanubi ne tun lokacin da suke 'yan yara.''

Sa'annan ne Allah ya yi bakan gizo na fari, ya zama alamar alkawarinsa. A dukkan lokacin da bakan gizo ya bayyana a sararin sama, Allah zai tuna abinda yayi alkawari, haka kuma mutanensa.

Related information

Words of Life - Audio gospel messages in thousands of languages containing Bible based messages about salvation and Christian living.

Free downloads - Here you can find all the main GRN message scripts in several languages, plus pictures and other related materials, available for download.

The GRN Audio Library - Evangelistic and basic Bible teaching material appropriate to the people's need and culture in a variety of styles and formats.

Choosing the audio or video format to download - What audio and video file formats are available from GRN, and which one is best to use?

Copyright and Licensing - GRN shares it's audio, video and written scripts under Creative Commons