unfoldingWord 25 - Shaidan ya jarabci Yesu
![unfoldingWord 25 - Shaidan ya jarabci Yesu](https://static.globalrecordings.net/300x200/z40_Mt_04_04.jpg)
Zusammenfassung: Matthew 4:1-11; Mark 1:12-13; Luke 4:1-13
Skript Nummer: 1225
Sprache: Hausa
Zuschauer: General
Zweck: Evangelism; Teaching
Features: Bible Stories; Paraphrase Scripture
Status: Approved
Skripte dienen als grundlegende Richtlinie für die Übersetzung und Aufnahme in anderen Sprachen. Sie sollten, soweit erforderlich, angepasst werden, um sie für die jeweilige Kultur und Sprache verständlich und relevant zu machen. Einige der verwendeten Begriffe und Konzepte müssen unter Umständen ausführlicher erklärt oder sogar ersetzt oder ganz entfernt werden.
Skript Text
![](https://static.globalrecordings.net/300x200/z40_Mt_04_01.jpg)
Nan da nan bayan an yi wa Yesu baftisma, Ruhu Mai Tsarki ya bishe Yesu zuwa jeji, in da ya yi azumi kwanaki da dare arba'in, sai Shaidan ya zo wurin Yesu ya jarabce shi domin ya yi zunubi.
![](https://static.globalrecordings.net/300x200/z40_Mt_04_02.jpg)
Shaidan ya jarabci Yesu yana cewa, in kai ne dan Allah, ka mai da duwatsun nan gurasa, don ka ci
![](https://static.globalrecordings.net/300x200/z40_Mt_04_03.jpg)
Yesu amsa ya ce, "A rubuce ya ke a kalmar Allah, 'Mutane basu bukatar gurasa kawai don su rayu, amma suna bukatar kowace kalma da Allah yake fada!"'
![](https://static.globalrecordings.net/300x200/z40_Mt_04_04.jpg)
Sa'annan Shaidan ya dauki Yesu ya kai shi saman haikali a wurin da ya fi tsawo duka, ya ce masa, "In kai ne dan Allah ka yi tsalle daga nan zuwa kasa, domin a rubuce yake, 'Allah zai umurci mala'ikunsa su tallafe ka domin kada kafanka ya yi tuntube da dutse.'''
![](https://static.globalrecordings.net/300x200/z40_Mt_04_05.jpg)
Amma Yesu ya amsa wa Shaidan da abinda aka rubuta daga cikin Nassi. Ya ce, "A kalmar Allah, ya umurci mutanensa, 'Kada ku gwada Ubangiji Allahn ku."'
![](https://static.globalrecordings.net/300x200/z40_Mt_04_06.jpg)
Sai Shaidan ya nuna wa Yesu dukkan mulkokin duniya da dukkan daukakarsu kuma ya ce, "Zan baka dukkan wannan, idan ka rusuna ka yi mani sujada."
![](https://static.globalrecordings.net/300x200/z40_Mt_04_07.jpg)
Yesu amsa "Rabu da ni, shaidan! A kalmar Allah ya umurci mutanensa, 'Ku yi wa Ubangiji Allahn ku sujada shi kadai kuma za ku bauta wa"'
![](https://static.globalrecordings.net/300x200/z40_Mt_04_08.jpg)
Yesu bai fada cikin jerabobin Shaidan ba, saboda haka Shaidan ya rabu da shi. Sai mala'iku suka zo suka yi wa Yesu hidima.