unfoldingWord 28 - Saurayi Shugaba Mai arziki

unfoldingWord 28 - Saurayi Shugaba Mai arziki

Omrids: Matthew 19:16-30; Mark 10:17-31; Luke 18:18-30

Script nummer: 1228

Sprog: Hausa

Publikum: General

Genre: Bible Stories & Teac

Formål: Evangelism; Teaching

Bibel citat: Paraphrase

Status: Approved

Scripts er grundlæggende retningslinjer for oversættelse og optagelse til andre sprog. De bør tilpasses efter behov for at gøre dem forståelige og relevante for hver kultur og sprog. Nogle anvendte termer og begreber kan have behov for mere forklaring eller endda blive erstattet eller helt udeladt.

Script tekst

Wata rana, wani saurayi mai arziki shugaba ya zo wurin Yesu, ya yi masa tambaya, "Malam Managarci me zan yi domin in sami rai madawwami?'' Yesu ya ce masa, ''Don me ka kira ni 'managarci'? Managarci daya ne, shine Allah. Amma Idan kana so ka sami rai madawwami, kayi biyayya da dokokin Allah.''

Yayi tambaya, ''Wadanne ne nake bukata in yi biyayya da su?'' Yesu ya amsa, ''Kada ka yi kissan kai. Kada ka yi zina. Kada ka yi sata. Kada ka yi karya. Ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka, sannan ka kaunaci makwabcin ka kamar yadda ka ke kaunar kanka.''

Amma saurayin ya ce, ''Na yi biyayya da dukkan wadannan dokokin tun ina dan yaro. Me nake bukata kuma in yi domin in rayu har'abada?'' Yesu ya kalle shi ya kaunace shi.

Yesu ya amsa, ''Idan kana so ka zama cikakke, to, ka je ka sayar da dukkan mallakar ka, ka ba wa talakawa kudin, za ka sami dukiya a sama. Sa'annan ka zo ka bi ni.''

Da saurayin ya ji abin da Yesu ya fada, sai ya cika da bakin ciki, domin shi mai arziki ne sosai, kuma bai so ya ba da dukkan mallakarsa ba. Sai ya juya ya tafi daga wurin Yesu.

Sai Yesu ya ce wa almajiransa, "Yana da wuya kwarai ga mutane masu arziki su shiga mulkin Allah! I, ya fiye sauki rakumi ya shiga ta ramin allura, da mai arziki ya shiga mulkin Allah.''

Sa'anda almajiran suka ji abin da Yesu ya fada, sai suka yi mamaki suka ce, "To wanene zai sami ceto?''

Yesu ya dubi almajiran , ya ce, ''Ga mutane wannan ba shi yiwuwa, amma da Allah kome mai yiwuwa ne.''

Bitrus ya ce wa Yesu, ''Mun bar kome mun bi ka, me zai zama sakamakon mu?''

Yesu ya amsa, ''Duk wanda ya bar gidaje, 'yan'uwa maza, da mata, uba da uwa, da 'ya'ya ko mallaka saboda ni, zai sami sama da ribi 100, ya kuma sami rai madawwami. Amma dayawa dake na farko za su zama na karshe, kuma wadanda ke na karshe za su zama na farko.''

Relateret information

Free downloads - Here you can find all the main GRN message scripts in several languages, plus pictures and other related materials, available for download.

The GRN Audio Library - Evangelistic and basic Bible teaching material appropriate to the people's need and culture in a variety of styles and formats.

Copyright and Licensing - GRN shares it's audio, video and written scripts under Creative Commons

Choosing the right audio or video format - What audio and video file formats are available from GRN, and which one is best to use?