unfoldingWord 14 - Yawo acikin Jeji

unfoldingWord 14 - Yawo acikin Jeji

概要: Exodus 16-17; Numbers 10-14; 20; 27; Deuteronomy 34

文本编号: 1214

语言: Hausa

听众: General

类型/流派: Bible Stories & Teac

目的: Evangelism; Teaching

圣经摘录: Paraphrase

状态: Approved

脚本是翻译和录制成其他语言的基本指南,它们需要根据实际需要而进行调整以适合不同的文化和语言。某些使用术语和概念可能需要有更多的解释,甚至要完全更换或省略。

文本正文

Bayanda Allah ya fada wa isra'ilawa dokokin da yake so su yi biyayya da su a matsayin alkawarin sa da su, suka tafi daga dutsen Sina'i. Allah ya fara jagorar su zuwa yankin kasar alkawari, wanda kuma ake kira kan'ana. Al'amudin girgije na tafiye a gabansu zuwa kan'ana su kuma suna biye da shi.

Allah yayi wa Ibrahim, Ishaku, da Yakubu alkawari cewa zai bada kasar alkawari ga zuri'ar su, amma yanzu akwai kungiyoyin mutane da yawa dake zaune a wurin. Ana kiran su kan'aniwa. Kan'aniwa basu bauta ko su yi biyayya da Allah ba. Suna bautar allolin karya kuma suna yin miyagun abubuwa da yawa.

Allah ya cewa Isra'ilawa, "Lalle ne ku kawar da dukkan Kan'aniwa acikin kasar alkawari. Kada ku yi yarjejjeniyar salama da su kuma kada ku aure su. Lelle ne ku hallakar da dukkan gumakunsu gabaki daya. Idan ba ku yi biyayya da ni ba, zaku bauta ma gumakunsu a maimako na."

Sa'anda Isra'ilawa suka iso gabar Kan'ana, Musa ya zabi mutum goma sha biyu, daya daga kowace kabilar Isra'ila. Ya basu umurni su je lekan asirin kasar su kuma gani yadda ta ke. Su kuma dubi yanayin Kan'aniwa su gani ko suna da karfi ko kasassu.

Mutanen nan goma sha biyu suka yi tafiya cikin Kan'ana kwana arba'in sa'an nan suka komo. Suka fada wa jama'ar, "Kasar na da albarka kuma ga yawan anfani!" Amma goma daga cikin masu lekan asirin suka ce, "Birnin na da karfin gaske kuma mutanen katti ne! Idan muka kai masu hari, tabbas zasu fi karfin mu kuma su kashe mu!"

Nan take Kalibu da Joshua, biyu daga cikin masu lekan asirin, suka ce, "Gaskiya ne mutanen Kan'ana dogi ne kuma karfafa, amma tabbas za mu sha karfin su, Allah zai yi yaki amadadin mu!"

Amma mutanen basu saurari Kalibu da Joshua ba. Suka yi fushi da Musa da Haruna suna cewa, "Me yasa kuka kawo mu wannan mummunar wuri? Da ma mun zauna a Masar maimakon a kashe mu cikin yaki kuma a maida matanmu da yayan mu bayi." Mutanen suna so su zabi wani shugaba dabam wanda zai komar da su Masar.

Allah ya husata kwarai har ma ya zo alfarwar saduwa. Allah yace, "Domin kunyi tawaye agare ni, dukkan mutane zasu yi famar yawo a daji. Banda Joshua da Kalibu, kowane daya dake shekara ashirin ko fiye zai mutu acan kuma ba zai taba shiga kasar alkawarin ba."

Da mutanen suka ji haka, suka tuba don sunyi zunubi. Suka dauki kayan yakinsu suka tafi domin su yaki mutanen Kan'ana. Musa kuwa ya gargade su kada su je domin Allah baya tare da su, amma basu saurare shi ba.

Allah bai tafi tare da su zuwa yakin ba, saboda haka aka yi nasara akan su kuma aka kashe da yawa acikin su. Sa'annan Isra'ilawa suka juya wa Kan'ana baya kuma su ka yi faman yawo a daji har shekaru arba'in.

Cikin shekaru arba'in da mutanen Isra'ila suka yi suna yawo a daji, Allah yana yi masu tanadi. Allah ya basu gurasa daga sama, da ake kira "Manna." Ya kuma aiko da yan tsalwa (wanda suke kananan tsuntsaye) a cikin taronsu domin su sami nama su ci. Cikin dukkan lokacin nan, Allah ya kare kayakinsu da takalmansu daga kodewa.

Allah kuwa cikin al'ajibinsa ya basu ruwa daga dutse. Amma duk da haka, mutanen Isra'ila suka yi gunaguni game da Allah da Musa. Duk da haka, adalcin Allah bisa alkawarinsa ga Ibrahim, da Ishaku da Yakubu bai sake ba.

Wani lokaci sa'adda mutanen suka rasa ruwa, Allah ya ce wa Musa, "Yi magana da dutse, ruwa kuwa zai fito daga ita." Amma Musa bai girmama Allah agaban dukkan mutanen ba ta wurin buga dutsen sau biyu da sanda amaimakon magana da ita. Ruwa kuwa ya fito daga dutsen domin kowa ya sha, amma Allah yana fushi da Musa kuma yace, "Bazaka shiga kasar alkawarin ba."

Bayan da Isra'ilawa suka yi ta zagaya acikin daji har shekaru arba'in, dukkan wadanda suka yi tawaye ga Allah sun mutu. Sa'annan Allah ya jagoranci mutanen zuwa iyakar kasar alkawari kuma. Musa kuwa ya tsufa sosai, sai Allah ya zabi Joshua ya taimake shi da shugabantar mutanen. Allah kuwa yayi wa Musa alkawari da cewa wata rana, zai aiko da wani annabi kamar Musa.

Sa'annan Allah ya ce wa Musa ya haura saman dutsen domin ya kalli kasar alkawarin. Musa kuwa ya kalla kasar alkawarin amma Allah bai yarda masa ya shiga ba. Sa'annan Musa ya mutu, Isra'ilawa kuwa suka yi makokinsa har kwana talatin. Joshua kuwa ya zama sabon shugabansu. Joshua shugaba ne nagari domin ya dogara kuma yana biyayya ga Allah.

相关信息

人生箴言 - GRN提供几千种语言的福音音频信息,包含圣经信息,救赎和基督徒生活。

免费下载 - 免费下载传福音及发展教会所用的录音、图片、文本和其他相关资料。内容包括福音与圣经故事,并已被翻译成上千种语言。

环球录音网音频图书馆 - Mp3,CD和磁带格式的福音材料和圣经教学材料,满足人们不同文化的需求。录音材料的形式多样,包括简单的圣经故事,福音信息,经文朗诵和歌曲。

Choosing the audio or video format to download - What audio and video file formats are available from GRN, and which one is best to use?

Copyright and Licensing - GRN shares it's audio, video and written scripts under Creative Commons